Limami Ya Kalli Bola Tinubu, Ya Yi Masa Wasu Addu'o'i a gaban Manyan Kasa a Abuja
- Babban limami a masallacin kasa, Farfesa Luqman Zakariyah ya yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu addu'o'i bayan sallar Juma'a a yau
- Limamin ya yi wa shugaban kasa addu'ar samun nasara a mulkinsa yayin daura auren 'ya'yan karamin ministan tsaro, Bello Matawalle
- Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya sanya albarka a cikin wadannan aurarraki da aka daura, ya ba ma’auratan zaman lafiya a rayuwarsu ta aure
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sha ruwan addu'o'i a wurin daura auren 'ya'yan karaminin ministan tsaro, Bello Matawalle.
Farfesa Luqman Zakariyah, limamin da ya jagoranci daurin auren ’ya’yan Bello Matawalle, a ranar Juma’a, ya bayyana Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin uba ga kowa.

Source: Twitter
Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X da yammacin yau Juma'a.
Sanarwar ta ce babban limamin masallacin ya yi addu’a da fatan mulkin Shugaba Bola Tinubu ya zama sanadin dawo da fata ga marasa galihu a cikin al’umma.
Farfesa Zakariyah ya gudanar da wadannan addu’o’i ne yayin da Shugaba Tinubu ya halarci taron daurin auren ’ya’yan Matawalle da aka yi a Masallacin Kasa da ke Abuja.
Shugaban kasar São Tomé and Príncipe, Carlos Manuel Vila Nova, na daya daga cikin manyan baki da suka halarci daura auren.
Addu'o'in da limamin ya yi wa Tinubu
Da yake yi wa Shugaba Tinubu addu'a, limamin masallacin ya ce:
"Muna rokon Allah Madaukakin Sarki ya ba shugabanmu, wanda yake wakiltar kowa, kuma uba ga daukacin amare da ango, lafiya mai dorewa.
"Haka kuma muna rokon Allah ya ba shugabanmu tsawon rai, arziki, da nasara a lokacin mulkinsa. Muna addu’ar cewa zamaninsa ya kawo fata ga marasa galihu."
'Ya'yan Matawalle 9 da aka daura wa aure
Matawalle, wanda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara ne, ya bada auren ’ya’yansa mata guda biyar, Maryam, Safiyya, Farida, Nana Firdausi, da Aisha.
Haka kuma, ’ya’yansa maza guda biyar,Ibrahim, Abdul Jalal, Surajo, Bello, da Fahad, su ma an daura masu aure a masallacin.
Shugaba Tinubu ne ya karbi amaren a madadin iyalan Matawalle zuwa cikin sabuwar rayuwarsu ta iyali

Source: Twitter
An yi wa ma'aurata addu'ar zaman lafiya
Limamin ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya sanya albarka a cikin wadannan aurarraki da aka daura, ya ba ma’auratan zaman lafiya a rayuwarsu ta aure,, sannan ya albarkaci iyayensu da kakanninsu.
Taron ya samu halartar Gwamnonin jihohi, mambobin Majalisar Tarayya, mambobin Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), Hafsoshin Tsaro, wakilan kasashen waje, sarakuna, malaman addini, da dubban masoya.
Jiga-jigan da suka halarci daura auren Matawalle
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na cikin wadanda suka halarci daurin auren yayan karamin ministan tsaro Bello Matawalle a babban masallacin kasa dake Abuja.
Daurin auren, wanda aka yi shi bayan sallar Jumu'ar yau, 6 ga Fabrairu, 2026, ya samu halartar manyan jami'an gwamnati da kuma jiga-jiganƴan siyasar ƙasar nan.
Bayan Tinubu, sauran manyan baƙi da suka halarta sun haɗa da Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, da ministan tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya).
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

