Sojoji Sun Yi Lalata da Mata, Sun Tatsi Talakawa a Cross River? Gaskiya Ta Fito

Sojoji Sun Yi Lalata da Mata, Sun Tatsi Talakawa a Cross River? Gaskiya Ta Fito

  • Rundunar sojoji ta 13 Brigade ta musanta zargin fyade da karbar kudin jama'a da ake yi wa dakarunta a lokacin rikicin Alesi da Ochon
  • Binciken sojoji ya nuna cewa bidiyon dake yawo a yanar gizo karya ne kuma an shirya shi ne domin bata sunan rundunar soja a idon jama'a
  • Rundunar ta fada wa mazauna Cross Rivers matakin da za su iya dauka don mika koke-kokensu idan har akwai wani soja da ya ci zarafinsu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Rundunar sojin Najeriya, musamman shalkatar runduna ta 13 (13 Brigade), ta musanta wasu zarge-zarge da ke yawo a kafafen sada zumunta game da dakarunta.

Rundunar ta musanta zargin cewa dakarunta sun yi wa mata fyaɗe tare da karɓar kuɗin talakawa a lokacin rikicin ƙabilanci tsakanin Alesi da Ochon a jihar Cross River.

Kara karanta wannan

Minista ya dauko da zafi, ya fara shirin garkame ma'aikatan Abuja a gidan yari

Rundunar sojoji ta musanta cewa dakarunta sun yi wa mata fyade a Cross Rivers.
Wasu dakarun sojojin Najeriya suna taimakawa mutanen da suka kubutar da su daga 'yan bindiga. Hoto: @HQNigerianArmy
Source: Twitter

Sojoji sun ci zarafin mata a Cross Rivers?

Mataimakin daraktan hulɗa da jama'a na rundunar, Manjo Yemi Sokoya, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma'a, 30 ga Janairu, 2026, in ji rahoton Punch.

Sanarwar ta bayyana cewa waɗannan zarge-zarge, waɗanda aka yaɗa a wani bidiyo dake magana kan abubuwan da suka faru tun watan Satumban 2025, ƙarya ne tsantsa kuma ba su da tushe balle makama.

Bayan yaɗuwar bidiyon, rundunar sojin ta ƙaddamar da binciken gaggawa ta hanyar jami'an tsaron soja domin gano gaskiyar lamarin.

A karshen binciken, eundunar ta ce bincikenta ya nuna babu wani soja da ya ci zarafin mata ko yi masu fyaɗe. Haka kuma, ba a samu shaidar cewa sojoji sun tatsi kuɗi ko kwashe kayan jama'a ba.

Shirga ƙarya domin ɓata sunan soja

Major Sokoya ya jaddada cewa dakarun sojin sun yi aiki ne ƙarƙashin tsauraran dokoki domin maido da zaman lafiya, kuma rundunar ba ta wasa da batun keta haƙƙin bil'adama.

Kara karanta wannan

Birgediya Janar Sadiq: Bayanan da muka sani kan sojan da ake zargi da hannu a 'juyin mulki'

Rundunar ta bayyana cewa waɗannan zarge-zarge an shirya su ne da gangan domin ɓata sunan dakarun soji da kuma hana samar da zaman lafiya mai ɗorewa a yankunan Alesi da Ochon.

Sanarwar ta yi nuni da wani rahoto na ɗan jarida mai bincike, Efio Ita, wanda aka wallafa a ranar 24 ga Satumba, 2025, wanda ya nuna cewa an shirya bidiyon ne domin rage wa sojoji kwarjini a idon jama'a.

Rundunar soji ta bukaci al'ummar Cross River da sojoji suka ci zarafinsu su bi matakan da suka dace wajen shigar da korafi.
Taswirar jihar Cross River, inda aka yi zargin sojoji sun ci zarafin mata. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Gargaɗi ga masu yaɗa jita-jita

Ya zuwa yanzu, babu wani mutum da ya shigar da ƙara a hukumance tare da bayar da rahoton likita ko shaidar ƴan sanda da za su nuna cewa an aikata waɗannan laifuka a kansa.

Rundunar sojin ta gargaɗi jama'a da su daina yaɗa rahotannin da ba su tabbatar da gaskiyarsu ba, domin hakan na iya rura wutar rikici tsakanin al'umma.

Ta kuma buƙaci dukkan wanda yake da korafi na gaskiya da ya bi hanyoyin da suka dace na shari'a ko na rundunar soja domin shigar da ƙara maimakon yin amfani da kafafen sada zumunta wajen yaɗa ƙarya.

Ana kama sojoji kan cin zarafin farar hula

A wani labari, mun ruwaito cewa, wasu jami'an rundunar sojin kasar nan sun fusata shugabanninsu bayan an gano su na cin zarafin wani farar hula a Legas.

Kara karanta wannan

Jarumin Nollywood ya shiga hannu a kan zargin shirin juyin mulki

Wannan na zuwa ne bayan an dauki sojojin a bidiyo, inda aka rika ganin yadda sojojin su ka ci zarafin farar hula guda biyu a Badagry, Legas.

Rundunar sojojin Najeriya dai ta bayar da hakuri ga jama'ar da lamarin ya fusata, ta kara da cewa bincike ya yi nisa domin gano musabbabin abin da ya faru.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com