Lokaci Ya Yi: Matashi Ya Rasu yayin Atisayen Aikin Soja a Kaduna

Lokaci Ya Yi: Matashi Ya Rasu yayin Atisayen Aikin Soja a Kaduna

  • Gwamnatin Gombe ta tabbatar da mutuwar wani matashi da ke neman aikin soja yayin atisaye a sansanin Zaria
  • An ce marigayin da ya rasu ɗan Gombe ne wanda ya rasa ransa bayan gajerar jinya a yayin horaswar Sojojin Najeriya
  • Gwamnatin jihar ta miƙa ta’aziyya, tana roƙon Allah ya gafarta masa kuma ya saka masa da Aljannar Firdausi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Gombe - Gwamnatin Jihar Gombe ta tabbatar da rasuwar wani matashi a jihar Kaduna da ke karbar horon aikin soja.

Marigayin mai suna Ibrahim Nazifi ya rasu yayin atisaye a sansanin horaswa na Sojojin Najeriya da ke Zaria a jihar Kaduna.

Gwamnatin Gombe ta sanar da mutuwar matashi mai karbar horaswar aikin soja
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe. Hoto: Isma'ila Uba Misilli.
Source: Facebook

Matashi ya mutu yayin atisayen soja a Kaduna

Hakan na cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Tsaro da Hulɗar Gwamnati, Ambasada Yusuf Danbayo, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Bello Turji ya firgita a cikin daji, yana gudun neman tsira zuwa wurare

Marigayin yana cikin rukuni na farko na matasan da suka yi nasarar shiga aikin soja daga Jihar Gombe, ƙarƙashin shirin 'Nigerian Army Regular Recruit Intake' (NA RRI 90).

Yusuf Danbayo ya ce Ibrahim Nazifi ya rasu ne bayan ya yi gajerar jinya a sansanin horaswar da ake ci gaba da yi.

Gwamnatin Gombe ta bayyana cewa marigayin ɗan asalin ƙauyen Buba Bani ne da ke Kashere a ƙaramar hukumar Akko, tare da lambar neman aikin soja 90RRI-GO-9017726.

Ya ce:

“Cikin matuƙar baƙin ciki da kaskantar da kai ga ƙaddarar Allah Maɗaukaki, nake sanar da rasuwar Ibrahim Nazifi, ɗaya daga cikin matasanmu masu cike da buri da ke samun horaswa a sansanin Sojojin Najeriya da ke Zariya.”
Matashi mai neman aikin soja ya mutu a Kaduna
Hafsan sojojin Najeriya, Laftanar-janar Waidi Shaibu. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Facebook

Gwamnatin Gombe ta yi ta'aziyyar mutuwar matashin

Danbayo ya bayyana marigayin a matsayin matashi mai kishin ƙasa wanda ya amsa kiran hidimtawa Najeriya, yana mai cewa rasuwar tasa ta girgiza iyalinsa, gwamnatin Jihar Gombe, al’ummar ƙaramar hukumar Akko da ma jihar baki ɗaya.

Ya miƙa ta’aziyyar gwamnatin jihar ga iyalan mamacin, ‘yan uwa, abokai da takwarorinsa, yana roƙon Allah ya gafarta masa kura-kuransa.

Kara karanta wannan

Takarar 2027: Yadda ake son tada rikici a ADC da matakin da Atiku ya dauka

“Wannan babban rashi ba iyalinsa kaɗai ya shafa ba, har da daukacin al’ummar Jihar Gombe da masu yi masa fatan alheri.
“Muna roƙon Allah Maɗaukaki ya gafarta masa, ya karɓi kyawawan manufofinsa da ƙoƙarinsa a matsayin ibada, kuma ya saka masa da Aljannar Firdausi.”

- In ji Danbayo

Danbayo ya ƙara da cewa wannan lamari tuna ce ga kowa cewa rayuwa ba ta dawwama, domin kowane rai sai ya ɗanɗana mutuwa, kuma ga Allah ne komawar ƙarshe take.

Sojoji sun musanta tilasta wa matasa aikin soja

A baya, kun ji cewa rundunar sojojin Najeriya ta fitar da sanarwa, domin wayar da kan al'umma kan jita-jitar cewa za ta tilasta wa matasa shiga aikin soja a kasar.

An danganta jita-jitar da cewa Laftanar-janar Waidi Shuaibu ne ya yi ikirarin tilasta matasa shiga soja, sai dai rundunar ta fito ta karyata rahoton.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta jawo martani daga jama’a, inda wasu suka nemi sojoji su maida hankali kan matsalolin tsaro da ya addabi mutane.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.