Yajin Aiki: Kotu Ta ba da Umarnin Wucin Gadi a Shari'ar Gwamnati da Likitoci

Yajin Aiki: Kotu Ta ba da Umarnin Wucin Gadi a Shari'ar Gwamnati da Likitoci

  • Babbar kotun masana'antu dake Abuja ta dakatar da kungiyar likitoci masu neman kwarewar aiki daga shiga yajin aiki a mako mai zuwa
  • Mai shari'a E. D. Subilim ya bayar da wannan umarni ne bayan gwamnatin tarayya ta shigar da korafi domin hana likitocin janye ayyukansu
  • Likitocin sun yi barazanar fara yajin aikin ne saboda zargin rashin gaskiyar gwamnati wajen aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a bara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Babbar Kotun Masana'antu da ke Abuja ta yanke wani hukuncin wucin gadi a ranar Juma’a, 9 ga Janairu, 2026, na dakatar da likitoci daga shiga yajin aiki.

Wannan hukunci ya hana likitocin da ke neman kwarewar aiki (NARD) shiga yajin aikin da suka shirya farawa daga ƙarfe 12:00 na daren ranar Litinin, 12 ga Janairu, 2026.

Kara karanta wannan

An yanke wa wani 'dan Najeriya hukuncin kisa a kasar waje, za a rataye shi

Kotu ta hana likitoci shiga yajin aiki bayan gwamnati ta shigar da korafi
Ma'aikaciyar asibiti ta jingina da gwiwarta da Shugaba Bola Tinubu a wajen taro. Hoto: Getty Images, @officialABAT/X
Source: Getty Images

Kotu ta saurari karar gwamnati da likitoci

Mai shari'a E. D. Subilim ne ya yanke wannan hukuncin biyo bayan ƙarar da gwamnatin tarayya da babban lauyan kasa suka shigar, in ji rahoton The Nation.

Wannan takaddama ta samo asali ne bayan da likitocin asibitin mahaukata na Aro da ke Abeokuta, da sauran rassan ƙungiyar ta NARD, suka bayyana aniyar tsunduma cikin yajin aikin sai baba ta gani.

Likitocin sun yi zargin cewa gwamnatin tarayya ta nuna “rashin gaskiya da halin ko-in-kula” wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka sanya wa hannu a baya.

Kotu ta hana likitoci shiga yajin aiki

Idan za a iya tunawa, Legit Hausa ta rahoto cewa likitocin sun dakatar da wani yajin aiki na kwanaki 29 a watan Nuwamban 2025 bayan alkawuran da gwamnati ta ɗauka, waɗanda yanzu suke zargin ba a cika su ba.

A cikin hukuncin da ya yanke, Mai shari'a Subilim ya haramta wa ƙungiyar NARD, shugabanninta, da dukkan mambobinta “kira, tsarawa, halarta, ko tsunduma cikin kowane irin yajin aiki, jinkirta aiki, ko zanga-zanga a wuraren aiki” har sai an kammala shari'ar gaba daya.

Kara karanta wannan

NNPP ta yi watsi da hukuncin kotu game da shugabancin jam'iyyar a Kano

Kotun ta bayyana cewa:

“An ba da umarnin dakatar da waɗanda ake ƙara, mambobinsu, ko wakilansu daga ɗaukar kowane mataki na shirya yajin aiki daga 12 ga Janairu, 2026, har sai an saurari ƙudurin da ke gaban kotu.”
Kotu ta ce likitoci ba za su shiga yajin aiki ba har sai an kammala sauraron shari'ar.
Wasu ma'aikatan asibiti da suka yi sahu sahu yayin daukar hoto. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

Abin da likitoci za su iya yi yanzu

Wannan umarni zai ci gaba da aiki har zuwa ranar 21 ga Janairu, 2026, lokacin da kotun za ta saurari hujjojin ɓangarorin biyu, in ji rahoton The Punch.

Gwamnati ta samu umarnin isar da takardun kotun ga likitocin a cikin kwanaki bakwai, yayin da su kuma likitocin ke da damar garzayawa kotun don neman soke wannan umarni idan suna da hujjoji masu ƙarfi.

Wannan mataki na kotu ya sa an samu annuri a fannin lafiyar kasar, inda ake fargabar durƙushewar asibitocin gwamnati idan har likitocin suka janye aiki.

NARD: Likitoci za su shiga yajin aiki

Tun da fari, mun ruwaito cewa, Kungiyar likitoci ta NARD ta sanar da shawarar da ta ɗauka na komawa yajin aikin sai baba ta gani a fadin kasar nan.

Kara karanta wannan

Sojoji sun raraka 'yan fashi da suka tare jama'a a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Likitocin sun ce daga ranar 12 ga watan Janairun shekarar da muke ciki, mambobin kungiyar za su janye aiki daga kowanne asibiti na fadin Najeriya.

NARD ta kuma ba da umarnin gudanar da zanga-zangar lumana a dukkan asibitoci 91 da ke ƙarƙashin ƙungiyar a faɗin ƙasar nan don nuna fushinsu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com