Jirgin Saman Sojoji Ya Yi Hatsari a Kokarin Yaki da ’Yan Ta’adda a Niger

Jirgin Saman Sojoji Ya Yi Hatsari a Kokarin Yaki da ’Yan Ta’adda a Niger

  • Rahotanni sun tabbatar da cewa jirgin yaki marar matuƙi na Rundunar Sojojin Sama ya faɗi a dajin jihar Niger
  • Hatsarin ya faru ƙasa da saoi 48 bayan ’yan ta’adda sun kashe manoma biyu tare da ƙona gidaje 13 a jihar
  • Rundunar Sojojin Sama ta ce babu asarar rayuka, kuma ayyukan yaƙi da ta’addanci na ci gaba ba tare da tangarɗa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kwantagora, Niger - Jirgin sama marar matuƙi na Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya (NAF) ya yi hatsari a wani daji a jihar Niger.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa an samu hatsarin ne a dajin Zangata da ke Ƙaramar Hukumar Kontagora, a Jihar Niger.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya tara 'yan Kwankwasiyya a;hali Abba na shirin hada kai da Ganduje a APC

Jirgin sojoji marar matuki ya fadi a Niger
Jirgin sojoji marar matuki. (An yi amfani da hoton ne domin misali kawai). Hoto: VCG/VCG.
Source: Getty Images

Yadda 'yan bindiga suka farmaki mutane a Niger

Lamarin ya faru ne ranar Juma’a 2 ga watan Janairun 2026 da yamma, jim kaɗan bayan hare-haren ’yan ta’adda a ƙauyukan Goro da Gebe na Ƙaramar Hukumar Agwara, cewar Aminiya.

Yayin harin, an ce maharan sun kashe manoma biyu tare da ƙona aƙalla gidaje 13 wanda ya tayar da hankulan al'ummar yankin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ƙauyukan da aka kai harin na kan iyaka tsakanin Borgu da Agwara, kuma ana zargin maharan sun tsere zuwa Jihar Neja ne daga Kwara bayan matsin lambar da sojoji suka musu.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kutsa fada da karfi da dare, sun sace Sarki da 'dansa

Wani mazaunin Kontagora, Zakari Adamu, ya ce jami’an tsaro ciki har da sojoji da ’yan sanda sun garzaya wurin da lamarin ya faru, amma a lokacin ba a tabbatar da irin ɓarnar da jirgin ya yi ko asarar rayuka ba.

Jirgin sojoji marar matuki ya yi hatsari a Niger
Taswirar jihar Niger da jirgin sojoji ya fadi. Hoto: Legit.
Source: Original

Martanin rundunar sojoji kan lamarin

Rundunar Sojojin ta tabbatar da faruwar hatsarin, inda ta bayyana cewa jirgin ya rasa sadarwa da cibiyar kulawa bayan an tura shi domin ci gaba da ayyukan yaƙi da ta’addanci.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Air Commodore Iya Komodo Ehimen Ejodame, ya fitar, rundunar ta ce babu wanda ya rasa ransa sakamakon hatsarin, cewar Sahara Reporters.

Ejodame ya ƙara da cewa an ɗauki matakan gaggawa domin gano jirgin tare da haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da tsaro da kuma aikin ceto.

Kara karanta wannan

Albishir da Gwamna Radda ya yi ga al'ummar Katsina game da ta'addanci

Ya bayyana cewa tuni aka gano jirgin, kuma ƙwararrun injiniyoyi sun fara tantance dalilin hatsarin tare da aikin dawo da shi bisa ƙa’idojin tsaro da aiki.

Rundunar Sojojin Sama ta jaddada cewa duk da faruwar hatsarin, ayyukan tsaro da yaƙi da ta’addanci na ci gaba a dukkan yankunan da ake fama da matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Jirgin sojoji ya yi hatsari a Niger

A baya, kun ji cewa wani jirgin sama na rundunar sojojin Najeriya ya gamu da hatsari a kusa da Karabonde, cikin Karamar Hukumar Borgu ta jihar Niger.

Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa matukan jirgin sun samu nasarar fita lafiya tun kafin jirgin ya kife.

Rundunar sojojin sama ba ta ce komai ba kawo yammacin na yau amma an fara yada bidiyoyin yadda jirgin ya kama da wuta bayan hatsarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.