Asiri Ya Tonu: 'Dan Majalisar Tarayya Ya ‘Gano’ Makirci a Dokar Sabon Haraji

Asiri Ya Tonu: 'Dan Majalisar Tarayya Ya ‘Gano’ Makirci a Dokar Sabon Haraji

  • 'Dan majalisa mai wakiltar mazabun Kebbe/Tambuwal, Abdussamad Dasuki, ya yi zargin sauya wasu bayanai na sabon dokar haraji
  • Hon. Dasuki ya yi zargin cewa an sauya wasu sassa na dokokin haraji bayan Majalisar Tarayya ta amince da su a kwanakin baya
  • 'Dan majalisar ya ce kwafin da aka fitar a hukumance ya bambanta da wanda da Majalisar Wakilai da Majalisar Dattawa suka amince

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Wani dan Majalisar Wakilai, Abdussamad Dasuki, ya ja hankalin ‘yan majalisa kan zargin cewa an yi sauye-sauye a dokokin haraji.

Hon. Dasuki ya ce an yi sauyin ne bayan Majalisar Tarayya ta amince da su wanda Bola Tinubu ya turo gabanta.

Dan majalisa ya zargi sauya dokokin haraji bayan amincewarsu a majalisa
Shugaba Bola Tinubu da Hon. Abdussamad Dasuki. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Abdussamad Dasuki.
Source: Twitter

Zargin dan majalisa kan dokokin haraji

'Dan majalisar ya bayyana haka ne a zaman majalisa a yau Laraba 17 ga watan Disambar shekarar 2025 da muke ciki, cewar rahoton Punch.

Kara karanta wannan

'An riga an rubuta sakamakon zaben 2027," Kalaman kakakin majalisa sun tada ƙura

Dasuki ya ce kwafin dokokin haraji da aka wallafa a hukumance ya bambanta da wanda da Majalisar Wakilai da Majalisar Dattawa suka daidaita kuma suka amince da ita.

Ya ce:

“Na tashi tsaye a yau saboda an take min hakki a matsayina na dan wannan muhimmiyar majalisa. Mun amince da wadannan dokokin haraji a wannan zaure. Na dauki lokaci na tsawon kwanaki uku ina duba kwafin da aka wallafa.”

Dasuki ya kara da cewa ya duba kundin kuri’u da shawarwarin Majalisar Wakilai, tare da komawa Majalisar Dattawa domin duba sigar da aka daidaita tsakanin bangarorin biyu.

Masanin tattalin arzikin ya ce abin da aka amince da shi a zauren majalisa ba shi ne abin da aka wallafa ba, kamar yadda The Guardian ta ruwaito.

“Na ba da kuri’ata, an kirga ta, amma yanzu ina ganin wani abu dabam."

- In ji shi.

Ya bukaci Kakakin Majalisar Wakilai da ya duba bambancin da ke tsakanin abin da aka amince da shi da abin da ke cikin kwafin da aka wallafa, yana mai cewa ‘yan Najeriya na ganin wani abu daban a hukumance.

Kara karanta wannan

An gano dalilin da ya sa Buhari ya sauya fasalin Naira daf da zaɓen Tinubu a 2023

Dan majalisa ya bukaci sake duba dokokin haraji da suka amince da su
Dan majalisar tarayya daga Sokoto, Hon. Abdussamad Dasuki. Hoto: Hon. Abdussamad Dasuki.
Source: Facebook

Abin Hon. Dasuki ke bukata daga majalisar

Dan majalisar na Kebbe/Tambuwal ya nemi a sake duba dokokin, yana mai cewa dukkan takardu su koma gaban Kwamitin da ke da alhakin haka domin a yi gyare-gyaren da suka dace.

Ya bayyana lamarin a matsayin keta kundin tsarin mulki da dokokin kasa.

“Wannan keta kundin tsarin mulki ne, kuma bai kamata wannan majalisa ta yi shiru ba."

- Cewar Dasuki

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce majalisar za ta binciki batun tare da daukar matakin da ya dace domin kare muradin kasa.

Haraji: Tinubu ya kwantar da hankulan mutane

An ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kara yin magana game da sababbin dokokin haraji da ake shirin farawa a sabuwar shekarar 2025.

Tinubu ya kwantarwa ’yan Najeriya hankulansu game da sababbin dokokin haraji da aka kawo domin ci gaban kasa da al'umma.

Shugaban ya yi karin haske cewa dokokin haraji za su amfani talakawa, masu ƙaramin albashi da ’yan kasuwa a Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.