Dalilan da Suka Sa Harkokin Kudi da Bankin Musulunci ke Karuwa a Fadin Najeriya

Dalilan da Suka Sa Harkokin Kudi da Bankin Musulunci ke Karuwa a Fadin Najeriya

  • Sheikh Bashir Aliyu Umar ya bayyana cewa tsarin harkokin bankin musulunci na kara karbuwa da yaduwa a Najeriya
  • Shugaban Majalisar Shari'ar Musulunci ya ce hakan na faruwa ne saboda tsaftar tsarin musulunci, wanda ya haramta riba
  • Shugaban BUK, Farfesa Haruna Musa ya ce bankin Summit ya shirya daukar daliban da suka gama karatu, mace da namiji aikin shekara biyar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya (SCSN), Dr. Bashir Aliyu Umar, ya yi magana kan gudanar da harkokin kudi da banki bisa tsarin Musulunci.

Sheikh Bashir Aliyu, babban malamin addinin musulunci mazaunin Kano, ya ce harkokin bankin musulunci na kara yaduwa a fadin Najeriya.

Bashir Aliyu.
Shugaban Majalisar Shari'ar Musulunci ta Najeriya, Dr. Bashir Aliyu Hoto: Dr. Bashir Aliyu
Source: Facebook

Dalilin karbuwar bankin Musulunci

A rahoton Daily Trust, babban malamin ya ce harkokin kudi da bankin musulunci na kara yaduwa ne saboda tsari mai kyau, mafita ga matsalolin kudi ba tare da cin riba ba, abin da Musulunci ya haramta.

Kara karanta wannan

'Kisan Kiristoci': Tawagar Amurka ta shigo Najeriya, ta yi magana da Ribadu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sheikh Bashir ya yi wannan bayani ne yayin da yake jawabi a wani taron bita na kwana biyu da Cibiyar Nazarin Al-Qur’ani ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta shirya.

Ya bayyana cewa yanzu Najeriya tana da bankuna biyar da ke tafiyar da al'amuransu bisa tsarin addinin Musulunci, inda ya ce harkokin bankunan ya kai darajar biliyoyin Daloli.

A cewarsa, bankin Musulunci na yaduwa ne saboda tsarin yana gina adalci, kwanciyar hankali da halastacciyar hulɗar kuɗi.

“Harkokin kuɗi na Musulunci na ƙara bunƙasa saboda tana tabbatar da adalci da kwanciyar hankali. An haramta riba ga Musulmi, kuma wannan tsari na samar da hanyoyin da suka dace da Shari’a,” in ji shi.

Bankin Summit ya ba jami'ar BUK dama

Shugaban BUK, Farfesa Haruna Musa, ya bayyana cewa Summit Bank zai bai wa dalibi namiji da daliba mace da suka fi kokari a fannnin harkokin kudi da bankin musululci na jami'ar damar aiki na tsawon shekaru biyar.

Kara karanta wannan

IBB ya gano matsalar Arewa, ya fadi dalilin rashin tsaro, talauci a yankin

Ya ce cibiyar nazarin Al-Qur’ani, wacce aka kafa a 2014, ta kudiri aniyar yaɗa koyarwar Al-Qur’ani, kuma jami’ar za ta ci gaba da ba ta goyon baya.

Sheikh Bashir Aliyu Umar.
Babban malamin addinin musulunci, Sheikh Bashir Aliyu Umar Hoto: Dr. Bashir Aliyu Umar
Source: Facebook

Shugaban cibiyar, Farfesa Ahmad Murtala, ya bayyana cewa an shirya wannan taron ne da nufin zurfafa fahimtar Shari’ar Musulunci a bangaren banki da harkar kuɗi.

Ya ce Jaiz Bank, Lotus Bank, TAJ Bank, Nur Takaful da wasu kamfanoni ne suka tallafa wajen daukar nauyin shirya taron.

“Wannan shi ne taro ma fi girma a harkar bankin Musulunci da wata cibiya a Arewacin Najeriya ta taba gudanarwa. Muna fatan maimaita irin wannan a sauran yankunan Najeriya.”

Bankuna sun kara kudin tes a Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa bankunan Najeriya sun sanar da sabon tsarin cire N6 daga asusun abokan hulɗarsu kan kowanne saƙon da aka turo ta wayar salula.

A baya dai ana cire N4 ne kan kowanne saƙon bayanin ma’amala, amma yanzu an ƙara N2 saboda ƙarin farashin da kamfanonin sadarwa suka yi.

Bankunan sun bayyana cewa saƙonnin na taimakawa kwastomomi su rika lura da duk wata mu’amalar kudi da ke faruwa a asusunsu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262