Jerin Sababbin Ministocin da Tinubu Ya Nada da Wadanda Ya Rabu da Su a 2025
Abuja, Nigeria - Yayin da shekarar 2025 ke bankwana, za mu duba sababbin fuska da aka samu da wadanda aka daina ganinsu a cikin ministocin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Shugaba Tinubu ya karbi mulki ne a ranar 29 ga watan Mayu, 2023 daga hannun tsohon shugaban kasa, marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya yi shekara takwas a mulki.

Source: Twitter
Bola Tinubu ya yi garambawul a 2024
Idan za ku iya tunawa a watan Oktoba, 2024, Shugaba Tinubu ya yi garambawul a majalisar zartarwa ta tarayya, inda ya sauke wasu ministoci kuma ya nada sababbi, cewar rahoton AIT.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A wannan lokaci, Tinubu ya kori ministoci biyar daga cikin 45, sannan kuma ya nada sababbi bakwai tare da canza wa wasu wurin aiki.
Ministocin biyar da aka kora sun hada da Ministar Harkokin Mata, Uju-Ken Ohanenye, Ministar Harkokin Yawon Bude Ido, Lola Ade-John da Ministan Ilimi, Tahir Mamman.
Sauran sune Karaminin Ministan Gidaje da Raya Biane, Abdullahi T. Gwarzo, da Ministan Harkokin Matasa, Jamila Ibrahim Bio.
Sai kuma sababbin ministoci bakwai da aka nada, Farfesa Nentawe Yilwatda, Muhammadu Dingyadi, Bianca Odumegu-Ojukwu, Jumoke Oduwole, Idi Maiha, Yusuf Abdullahi Ata da Suwaiba Ahmad.
Jerin ministocin da Tinubu ya nada a 2025
Bayan wannan, a 2025, Shugaba Tinubu ya kara yin gyare-gyare tare da nada sababbin ministoci sakamakon murabus din da wasu suka yi.
Bisa haka ne Legit Hausa ta tattaro muku ministocin da Shugaba Tinubu ya nada a shekarar da ke mana bankwana watau 2025. Ga su kamar haka:
1. Dr. Kingsley Tochukwu Ude (SAN)
A watan Oktoba, 2025, Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-Kirkire, Uche Nnaji ya yi murabus daga kujerarsa saboda zarge-zargen da ake masa na amfani da takardun karatu na bogi.
A wata sanarwa sa fadar shugaban kasa ta wallafa a shafin yanar gizo, Shugaba Tinubu ya amince da murabus din Nnaji, tare da yi masa fatan alheri a ayyukansa na gaba.

Source: Facebook
Daga bisani, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Dr. Kingsley Tochukwu Ude (SAN) daga jihar Enugu a matsayin wanda zai maye gurbin Nnaji.
Shugaban ya kuma tura wa Majalisar Dattawa sunan sabon ministan a watan Oktoba, 2025, inda bayan tantancewa ta amince da nadin Dr. Ude, kamar yadda Channels tv ta kawo.
2. Bernard Doro
Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Dr. Bernard Doro daga Jihar Filato a matsayin Minista domin maye gurbin Farfesa Nentawe Yilwatda, wanda ya zama shugaban jam'iyyar APC na kasa a watan Yuli, 2025.
Tinubu ya kuma tura sunan Dr. Doro ga Majalisar Dattawa a ranar 21 ga watan Oktoba, 2025, kuma bayan tantance shi, Majalisar ta amince da nadinsa.
Doro ya maye gurbin Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin Ministan Harkokin Jin ƙai da Kawar Talauci, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Source: Twitter
Fadar shugaban kasa ta tabbatar da cewa Tinubu ya rantsar da Dr. Kingsley Tochukwu Ude (SAN) da Dr. Bernard Doro a matsayin sabbabin ministoci da za su cike guraben da aka bari ba kowa.
Ministocin sun yi rantsuwar kama aiki a taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC), wanda aka gudanar ranar 6 ga watana Nuwamba, 2025 a zauren Majalisar da ke fadar shugaban kasa.
3. Janar Chirstopher Musa
A ranar Talata, 2 ga watan Disamba, 2025, Shugaba Tinubu ya nada tsohon hafsan tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya) a matsayin sabon Ministan Tsaron Najeriya.
Wannan mataki na zuwa ne sa'o'i kadan bayan Muhammad Badaru Abubakar ya yi murabus daga kujerarsa ta Ministan Tsaro.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X.

Source: Facebook
A cikin wata wasika da ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Bola Tinubu ya mika sunan Janar Musa a matsayin magajin Badaru Abubakar, wanda ya yi murabus a ranar Litinin.
Janar Musa, wanda zai cika shekaru 58 a ranar 25 ga Disamba, soja ne mai hazaka wanda ya yi aiki a matsayin Babban Hafsan Tsaro daga 2023 zuwa Oktoba 2025.
Ya lashe kyautar gwarzon sojoji ta Colin Powell Award a shekarar 2012, wanda ya nuna jarumta da jajircewar da yake da ita.
Tinubu ya nada sababbin jakadu 32
A wani rahoton, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya nada sababbin jakadu 32, wadanda za su wakilci Najeriya a kasashe daban-daban a duniya.
Tinubu ya aika wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu 32 domin tantancewa da tabbatarwa, kwanaki kadan bayan ya aika jerin farko na mutane uku.
Tsohon shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu na daya daga cikin fitattun mutanen da aka gani a sunayen da fadar shugaban kasa ta fitar.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng



