Bayan Ceto Ɗaliban Kebbi, An Ji Abin da Gwamna Nasir Ya Tattauna da Tinubu

Bayan Ceto Ɗaliban Kebbi, An Ji Abin da Gwamna Nasir Ya Tattauna da Tinubu

  • Gwamna Nasir Idris ya gana da Bola Tinubu a Abuja domin tattauna matsalolin tsaro da cigaba, tare da godewa gwamnati kan ceto dalibai
  • Kauran Gwandu ya bayyana matakan tsaro da ake aiwatarwa, ya kuma jaddada muhimman ayyukan ci gaba a noma, ilimi domin bunkasa jihar
  • Tinubu ya yaba da kokarin gwamna, ya kuma tabbatar da goyon bayan tarayya ga hadin gwiwar tsaro, leken asiri da gaggawar daukar matakai Kebbi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kebbi - Gwamnan Kebbi, Dr. Nasir Idris, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa da ke birnin Abuja.

Gwamnan ya hadu da Bola Tinubu ne domin tattauna kalubalen tsaro da muhimman shirin cigaba na jihar Kebbi.

Gwamna Nasir Idris ya gana da Tinubu a Abuja
Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris. Hoto @NasiridrisKG.
Source: Facebook

Hakan na cikin wata sanarwa da gwamnan ya fitar a shafin X a yau Asabar 29 ga watan Nuwambar 2025.

Kara karanta wannan

Martanin Barau da gwamnatin Kano ta nemi a cafke shi saboda zargin ingiza rashin tsaro

Gwamna Nasir Idris ya gana da Tinubu

Gwamnan ya gode wa Tinubu kan ceto dalibai 24 da ’yan bindiga suka sace daga makarantar sakandaren.

Gwamnan ya gabatar da bayani kan matsalolin tsaro, ya kuma bayyana matakan kariya da muhimman ayyukan noma, ilimi da kiwon lafiya domin cigaban jihar.

A cewarsa:

"Na yi wata muhimmiyar ganawa da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a Abuja, inda muka tattauna batun tsaron ƙasa da kuma nasarar ceto ’yan matan makarantar mu na Maga.
"Na yaba wa Shugaban Kasa bisa jagorancinsa da gaggawar matakin da ya dauka don ganin an dawo da su lafiya."
Gwamna Idris ya yabawa Tinubu kan tsaro
Gwamna Nasir Idris yayin ganawa da Bola Tinubu a Abuja. Hoto: @NasiridrisKG.
Source: Twitter

Gwamna ya yabawa Bello Matawalle

Gwamna ya yaba da goyon bayan Tinubu mara adadi da ƙoƙarinsa wajen tabbatar da tsaron Jihar Kebbi inda ya ce abin yabawa ne ƙwarai.

Har ila yau, Nasir Idris ya yaba da kokarin ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle duba da rawar da ya taka wurin ceto ɗaliban da aka sace.

Kara karanta wannan

Rashin tsaro: ADC ta jefa zafafan tambayoyi ga gwamnatin Tinubu

"Haka kuma, ina godiya ga Ministan Harkokin Tsaro na Jiha, Muhammad Bello Matawalle, bisa rawar da ya taka a aikin ceto, tare muke samun cigaba wajen tabbatar da tsaron jiharmu da ƙarfafa al’ummarmu."

- Nasir Idris

Abin da Tinubu ya ce ga Gwamna Idris

Taron ya mayar da hankali kan hadin gwiwar tsaro, leken asiri, gaggawar daukar mataki da aiki tare tsakanin jami’an jiha da tarayya domin rage barazana.

Tinubu ya yaba da kokarin gwamnan, ya kuma tabbatar da karin goyon bayan tarayya domin hanzarta aiwatar da muhimman shirye-shiryen cigaba a fadin Kebbi.

Gwamnan ya je tare da Ministan Kasafi da Tsare-tsare na Kasa, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, wanda ya mara masa baya a ziyarar Aso Villa.

Sojoji na binciken dakaru bayan sace daliban Kebbi

Kun ji cewa janyewar da sojoji suka yi daga makarantar GGCSS Maga a jihar Kebbi na ci gaba da shan suka inda wasu ke ganin akwai sakaci.

Gwamnatin Kebbi ta bukaci binciken sojojin domin gano dalilin da ya sa suka janye kafin harin da 'yan bindiga suka kai.

Wannan koken ya kai wajen hedkwatar tsaro ta kasa inda ta gayyaci sojojin da ke da alhakin gadin makarantar domin fara binciken lamarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.