An Saki Sunayen Dalibai 25 da Aka Sace a Kebbi bayan Kalaman 'Dan Majalisar Amurka

An Saki Sunayen Dalibai 25 da Aka Sace a Kebbi bayan Kalaman 'Dan Majalisar Amurka

  • Gwamnatin karamar hukumar Danko/Wasagu da ke jihar Kebbi ta karyata zargin cewa daliban da aka sace a Maga kiristoci ne
  • Shugaban karamar hukumar, Hon. Hussaini Aliyu ya bayyana zargin a matsayin karya mara tushe, ya ce duka daliban musulmai ne
  • Ya kuma saki jerin sunayen dalabai 25 da 'yan bindigan suka sace domin karyata ikirarin dan Majalisar Amurka, Riley Moore

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kebbi, Nigeria - Shugaban Karamar Hukumar Danko/Wasagu na jihar Kebbi, Hussaini Aliyu, ya karyata wani ikirari da aka danganta wa dan majalisar Amurka, Riley Moore.

Dan Majalisar Amurka ya yi zargin cewa wadanda yan bindiga suka yi garkuwa da su a harin da suka kai makarantar mata ta Maga a Kebbi duk kiristoci ne.

Makarantar Maga.
Hoton allon sanarwa na makarantar sakandiren yan mata da ke garin Maga a jihar Kebbi Hoto: NTA News
Source: Facebook

Da gaske kiristoci aka sace a Kebbi?

NTA News ta tattaro cewa shugaban karamar hukumar Danko/Wasagu, Hon Aliyu ya karyata wannan zargi, yana mai bayyana cewa dukkan yaran da aka sace Musulmai ne.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Sanatan Amurka ya taso gwamnati a gaba kan sace dalibai a Kebbi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma ayyana wannan magana a matsayin mara tushe kuma abin tada fitina, musamman a lokacin da gwamnati ta mayar da hankali kan ceto yaran cikin koshin lafiya.

Ya jaddada cewa Masarautar Zuru, wadda kauyen Maga ke karkashinta, tana da dogon tarihi na zaman lafiya tsakanin al’umma, kuma ba ta taba fuskantar rikicin addini ba.

Tuni dai gwamnatin Najeriya ta bai wa rundunar sojoji umarnin ceto daliban da aka sace cikin koshin lafiya domin su koma cikin iyalansu.

Sunayen daliban Kebbi 25 da aka sace

Don haka ya bukaci dan majalisar Amurka ya daina fitar da bayanan da ba a tabbatar da su ba, wadanda za su iya bata sunan Najeriya ko karya hadin kan kasa, in ji Premium Times.

Ciyaman din ya bayyana sunayen daliban da yan bindigar suka sace domin tabbatar da gaskiyar maganarsa. Ga sunayen kamar haka:

SS 2A

1. Fatima Sani Zimri

2. Hafsat Ibrahim

Kara karanta wannan

Remi Tinubu ta fadi halin kunci da ta shiga bayan sace dalibai mata a Kebbi

3. Nana Firdausi Jibril

4. Masauda Yakubu Romo

SS 2B

5. Hauwa Saleh

6. Hauwa’u Umar Imam

SS 3A da 3B

7. Salima Garba Umar

8. Salima Sani Zimri

9. Amina G. Umar

10. Rashida Muhammad Dingu

11. Saliha Umar

12. Aisha Usman

13. Jamila Iliyasu

14. Maryam Illiyasu

15. Najaatu Abdullahi

16. Zainab Kolo

JSS 3A

17. Surraya Tukur

18. Hafsat Umar Yalmo

19. Maryam Usman

20. Amina Illiyasu

21. Ikilima Suleman

JSS

22. Khadija Nazifi

23. Hauwa’u Iliyasu

24. Hauwa’u Lawali

25. Ummu Kulsum Abdulkarim.

Gwamnan Kebbi.
Hoton makarantar da aka sace yan mata da Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi Hoto: Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu
Source: Facebook

Dalibai mata 2 sun kubuta a Kebbi

A wani labarin, kun ji cewa dalibai mata biyu daga cikin daliban da aka sace daga makarantar sakandire ta yan mata, GGSS Maga, a jihar Kebbi, sun kuɓuta daga hannun ‘yan bindiga.

Harin sa yan bindiga suja kai makarantar ya janyo fargaba da ɗar-ɗar a yankin Danko Wasagu, inda ake ci gaba da neman sauran dalibai da aka yi garkuwa da su.

Kara karanta wannan

Gwamnonin Arewa sun fitar da matsaya kan daliban Kebbi da aka sace

Rahotani sun nuna cewa daliban guda biyu daga ciki sun gudo ne lokacin da ‘yan bindigar ke tursasa su shiga cikin dazuzzuka, inda suka yi ta gudu har zuwa gonaki a kusa da yankin.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262