Nnamdi Kanu: Wike Ya Fadi Sharadin Zama Shaidan Shugaban IPOB a Kotu

Nnamdi Kanu: Wike Ya Fadi Sharadin Zama Shaidan Shugaban IPOB a Kotu

  • Ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana damuwa game da sanya sunansa cikin wadanda za su ba da shaida a kotu
  • Wike ya ce ba zai bayyana a kotu a shari’ar shugaban kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu ba saboda kawai sunansa ya fito a jarida
  • Ministan ya ce zai halarci kotu ne kawai idan aka ba shi sammaci a hukumance, yana mai jaddada cewa dole ne ya mutunta umarnin kotu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike ya yi fatali da maganar zuwa kotu domin ba da shaida kan shari'ar Nnamdi Kanu.

Wike ya bayyana cewa ba zai bayyana a kotu a shari’ar shugaban IPOB din da ake tuhuma ba saboda kawai sunansa ya fito a jarida ba.

Wike ya fadi dalilin da ya sa ba zai ba da shaida kan Nnamdi Kanu ba
Nnamdi Kanu da ministan Abuja, Nyesom Wike. Hoto: STEFAN HEUNIS, Nyesom Wike.
Source: Getty Images

Yayin taron manema labarai a Abuja da Channels TV ta bibiya, Wike ya ce ba wanda ya ba shi takardar kiran kotu ko wata doka da ta bukaci ya bayyana.

Kara karanta wannan

Abin da Wike ya ce bayan yaɗa cewa Tinubu ya hana shi magana kan gwamnatinsa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da me ake tuhumar Nnamdi Kanu a kotu?

Mazi Kanu, wanda mutumin Najeriya ne da kuma ƙasar Birtaniya, yana fuskantar tuhumar ta’addanci wajen kira da yake yi na neman ’yancin kai ga yankin Kudu maso Gabas.

An fara kama shi a watan Satumban 2015 saboda shirye-shiryen rediyo da yake yi yana goyon bayan ballewar yankin Igbo daga Najeriya domin kafa ƙasar Biafra.

Daga baya an ba shi beli amma ya gudu daga ƙasar a 2017 bayan wani samame da sojoji suka kai garinsa na jihar Abia.

An sake cafke shi a 2021, kuma tun daga lokacin yana hannun hukumar DSS, daga nan shari’arsa ta shiga hannun alkalai huɗu na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, tare da sauye-sauyen lauyoyinsa masu kare shi.

Wike ya magantu kan ba da shaida a kotu kan Nnamdi Kanu
Tsohon gwamnan Rivers kuma ministan Abuja, Nyesom Wike. Hoto: Nyesom Wike.
Source: Facebook

Kanu: Abin da WIke ke jira daga kotu

Wike ya ce, zai bi umarnin kotu ne kawai idan an kira shi da sammaci na doka don bayar da shaida ko gabatar da hujja, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Gwamna ya kakaba haraji kan masu jana'za, aure da suna? An ji gaskiyar lamari

Ya ce:

“Ba saboda na ga sunana a jarida zan fara gudu ba. Idan kotu ta bukace ni da sammaci, dole ne na halarta."

Da aka tambaye shi dalilin da yasa Nnamdi Kanu ya lissafa sunansa cikin shaidu, Nyesom Wike ya ce shi kansa bai san dalili ba.

Ya ce shi bai taba magana da shi ba cewa yana son ya ba da shaida a kotu game da abin da ake tuhumarsa a kai.

“In ka ga Nnamdi Kanu, ka tambaye shi, me yasa ka saka sunana?’ Ban taba cewa ina son zama shaida ba.”

- Nyesom Wike

Me gwamnoni za su 'fada' a shari'ar Kanu?

Mun ba ku labarin cewa shugaban IPOB, Nnamdi Kanu ya fitar da jerin shaidu yayin da ya ke shirin kare kansa a shari’ar ta’addanci da gwamnatin Najeriya ke yi da shi.

An bayyana cewa a cikin jerin akwai tsofaffin ministoci, hafsoshin tsaro da gwamnoni da suka hada da Abubakar Malami, T.Y. Danjuma da Tukur Buratai.

Kara karanta wannan

Nnamdi kanu: An gano abin da Buratai, gwamnoni da wasu manyan kasa za su fada a kotu

Shaidun za su bayar da bayani kan yadda aka kama Kanu, yadda aka haramta IPOB, da kuma abubuwan da wasu batutuwa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.