Sauya Shekar Gwamnoni, Jagoran APGA Ya Zargi Majalisa da Zama 'Yar Amshin Shata
- Chekwas Okorie ya ce yawancin gwamnoni na tserewa zuwa APC saboda tsoron EFCC bayan karewar wa’adinsu a mulki
- Ya zargi majalisar tarayya da zama 'yar amshin shata, musamman wajen gaza hana sauya sheka ba bisa ka’ida ba tsakanin jam’iyyu
- A cewar jigon jam'iyyar ta APGA, 'yan majalisa na da damar wofantar da kujerar duk wanda ya fice daga jam'iyyar da ya ci zabe
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja – Tsohon shugaban jam’iyyar APGA, Chief Chekwas Okorie, ya bayyana dalilin da ya sa yawancin gwamnonin jam’iyyun adawa ke sauya sheka zuwa APC.
Chief Chekwas Okorie ya bayyana cewa gwamnonin adawa na tururuwar komawa APC saboda suna tsoron haduwa da hukumar EFCC bayan karewar wa’adinsu.

Source: Twitter
'Abin da ke sa gwamnoni shiga APC' - Okorie
A wata tattaunawa da jaridar Vanguard, Okorie ya bayyana cewa gwamnoni da dama na ganin shiga APC tamkar mafaka ce daga tuhumar rashawa da za su iya fuskanta daga hukumar EFCC bayan sun sauka daga mulki.
Chief Okorie ya ce yawancin wadannan gwamnoni sun yi amfani da girman mukam ansu wajen aikata laifuka da almundahana.
A cewarsa, sun yi hakan ne saboda sun san sashe na 308 na kundin tsarin mulki ya basu kariya daga gurfanar da su a kotu yayin da suke mulki.
“Suna jin tsoron tozarcin da EFCC za ta musu idan sun rasa kariyar ofis, shi ya sa suke guduwa zuwa jam’iyyar da ke mulki."
- Chief Chekwas Okorie.
Ya kara da cewa, wannan salon da gwamnonin jam'iyyun adawa ke amfani da shi na tserewa zuwa jam’iyya mai mulki bai taba tsare kowa daga tuhuma ba.
Gwamnoni na garari bayan kammala wa'adinsu
Jagoran na jam'iyyar APGA ya tuna yadda wasu daga cikin gwamnonin kasar nan da suka tsaya takarar majalisar dattawa bayan shekara takwas a kan mulki, suka sha kaye a zabe.
Okorie ya bayyana cewa, akalla gwamnoni shida da suka yi mulki tsawon shekaru takwas sun kasa lashe kujerar majalisar dattawa a zaben da ya gabata, inda ɗaya kacal cikin su ya samu mukami daga fadar shugaban kasa.
Ya soki tsarin siyasar Najeriya, yana mai cewa:
“Ba su da wani tabbacin samun wani mukami. Ire-iren halayensu ne ke lalata tsarin dimokuraɗiyya. Kuma ga majalisar dokoki ta kasa ta gaza cika nauyinta.”

Source: UGC
Jigon APGA ya caccaki 'yan majalisar tarayya
Chief Okorie ya zargi majalisar dokoki ta tarayya da zama “'yan amshin shata” na bangaren zartarwa ta kasa.
Ya ce ya kamata dokar kasa ta tilasta kowane dan siyasa da ya bar jam’iyyarsa rasa kujerarsa kai tsaye, sannan hukumar INEC ta gudanar da sabon zabe.
“Ta haka ne za mu tabbatar da gaskiya. Amma yanzu mutane na cin moriyar jam'iyyar da suka hau kujera su yada korenta, su sauya sheka zuwa jam'iyya mai mulki don kare kawunansu."
- Chief Chekwas Okorie.
Gwamnoni 3 za su koma jam'iyyar APC
A wani labarin, mun ruwaito cewa, akwai yiwuwar jam'iyyar APC za ta samu karin gwamnoni uku da za su baro tsagin adawa zuwa cikinta a makon nan.
Rahotanni sun gano sunayen gwamnoni biyu daga ciki, wadanda za su sauya sheka daga PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya.
Daga cikin waɗanda ake tsammani za su koma APC akwai Gwamna Peter Mbah na jihar Enugu da Gwamna Douye Diri na jihar Bayelsa, kuma za su koma tare da jama'arsu.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


