Jami'an Tsaro Sun Cafke Barawon da Ya Sato Motar Asibiti daga Kasar Nijar
- Dubun wani barawon mota ta cika bayan jami'an hukumar shige da fice ta kasa (NIS) sun yi caraf da shi a jihar Jigawa
- Jami'an na hukumar NIS sun cafke barawon ne bisa zargin sato wata motar asibiti daga Jamhuriyar Nijar mai makwabtaka da Najeriya
- Dubun barawon ta cika ne bayan ya shigo da motar asibitin zuwa iyakar Najeriya da Nijar, inda jami'an tsaro suka yi caraf da shi
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Jigawa - Jami’an hukumar shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Jigawa, sun samu nasarar cafke wani matashi bisa zargin sata.
Jami'an na hukumar NIS a Jigawa sun cafke matashin ne bisa zargin sato wata motar asibiti daga Jamhuriyar Nijar mai makwabtaka da Najeriya.

Source: Facebook
Jaridar Aminiya ta kawo rahoton cewa shugaban hukumar NIS na jihar Jigawa, Tahir Abdullahi Musa, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a birnin Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Yadda aka cafke barawon motar asibiti
Jami'an tsaron sun cafke matashin ne yayin da yake kokarin shigo da motar asibitin da ake zargin ya sato daga Jamhuriyar Nijar, zuwa Najeriya.
Shugaban na hukumar NIS ya bayyana sunan matashin da aka cafke a matsayin Yusif Bashir.
Tahir Abdullahi Musa ya ce an kama wanda ake zargin da motar asibiti kirar Toyota Land Cruiser mai lamba ONG-0777, bayan ya samu nasarar shigo da ita ta iyakar Babura da Jamhuriyar Nijar.
Wane mataki hukumar NIS za ta dauka?
Shugaban na NIS ya ce tuni hukumar ta fara shirye-shiryen sada shi da rundunar ’yan sandan jihar Jigawa.
Ya ce za a mika wanda ake zargin ne zuwa ga hannun 'yan sanda domin ci gaba da gudanar da bincike.
Hakazalika ya kara da cewa hukumar NIS za ta ci gaba da haɗa kai da sauran hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.

Source: Original
Karanta wasu labaran kan hukumar shiga da fice
- 'Yan bindiga sun sace matar babban jami'in gwamnati, suna neman miliyoyin Naira
- Gwamna ya karrama jami'in NIS da ya ki karbar N10m wajen bokan da aka kama
- An yi arangama a Niger, dan sanda ya dirkawa jami'ar hukumar NIS bindiga, an tsare wasu
- Bayanai sun fito da kotu ta garkame yan sanda 2 da jami'in hukumar NIS a Gombe
- Barazanar tsaro: An kama 'yan kasashen waje 165 da shirin kulla makirci a Najeriya
An kai jami'in hukumar NIS kotu
A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC, ta gurfanar da wani jami'in hukumar shige da fice ta kasa (NIS,), bisa zargin rashin gaskiya.
Ana zargin jam'in na hukumar NIS da karbar albashin da ya kai N17.6m daga wasu hukumomin gwamnati guda uku.
Hukumar ICPC ta kai Abubakar Mohammed Aseku gaban kotu bisa zargin cewa ya karbi albashin N17.6m daga ma’aikatu daban-daban a wani tsawon lokaci, lamarin da ya sabawa dokokin aikin gwamnati.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

