Farfesa Mahmood Yakubu Ya Sauka daga Mukamin Shugaban INEC

Farfesa Mahmood Yakubu Ya Sauka daga Mukamin Shugaban INEC

  • Farfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga matsayin shugaban hukumar zabe ta kasa watau INEC bayan karewar wa'adinsa na biyu
  • Yakubu ya mika ragamar shugabancin hukumar ga May Agbamuche, wacce za ta rike INEC kafin nadin sabon shugaba
  • Tun a shekarar 2015, marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya nada Mahmood Yakubu a matsayin shugaban INEC na kasa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa Mai Zaman Kanta (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya kammala wa'adinsa na shekaru 10 kamar yadda doka ta tanada.

A yau Talata, 7 ga watan Oktoba, 2025, Farfesa Yakubu ya mika ragamar jagorancin INEC ga May Agbamuche a matsayin mukaddashin shugabar hukumar.

Farfesa Mahmud Yakubu.
Hoton shugaban INEC mai barin gado, Farfesa Mahmood Yakubu. Hoto: @INECNigeria
Source: Facebook

Farfesa Mahmood Yakubu ya bar kujerar INEC

Channels tv ta ruwaito cewa Agbamuche ita ce babbar kwamishina mafi dadewa a aiki a hukumar zaben Najeriya.

Kara karanta wannan

Abin da Tinubu ya fada da Shugaban INEC ya ajiye aiki, ya ba shi kyautar sallama

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Farfesa Yakubu ya sanar da haka ne a ranar Talata yayin ganawarsa da kwamishinonin zaɓe na jihohi a hedikwatar INEC da ke Abuja.

Ya bukaci kwamishinoni da daraktocin INEC su bai wa Agbamuche cikakken goyon bayan har zuwa lokacin da za a naɗa sabon shugaban hukumar.

Hakan dai na nufin Farfesa Mahmud Yakubu ya bar kujerar shugaban hukumar INEC bayan ya kammala wa’adinsa biyu na tsawon shekaru 10.

Ana sa ran Shugaba Bola Tinubu zai naɗa wanda zai gaje shi nan ba da jimawa ba, bisa amincewar majalisar dattawa.

Yadda Yakubu ya kafa tarihi a hukumar INEC

Yakubu ya zama shugaban INEC ne a watan Nuwamba 2015 lokacin da tsohon shugaban ƙasa, Marigayi Muhammadu Buhari ya naɗa shi, watanni shida bayan hawansa mulki.

Ya kammala wa’adinsa na farko a shekarar 2020, inda daga bisani Shugaba Buhari ya sake naɗa shi karo na biyu, in ji rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

NAHCON ta fitar da sanarwa kan umarnin rage kudin Hajjin 2026 da Tinubu ya yi

Hakan ya sa Farfesa Mahmood Yakkubu ya zama mutum na farko da ya shugabanci hukumar zaben Najeriya watau INEC na tsawon wa'adi biyu.

Yakubu ya gaji Farfesa Attahiru Jega, inda a zamaninsa hukumar INEC ta gudanar da manyan zaɓuɓɓuka da dama, ciki har da na 2019 da kuma 2023.

Shugaba Tinubu zai nada shugaban INEC

A halin yanzu, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ke da ikon nada wanda zai gaji Farfesa Mahmood Yakubu tare da amincewar Majalisar Dattawa.

Wasu majiyoyi daga fadar shugaban kasa, sun nuna cewa Shugaba Tinubu ya fara karkata kan Farfesa Joash Ojo Amupitan, SAN, dan asalin jihar Kogi a matsayin wanda zai gaji Yakubu.

Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu.
Hoto. Farfesa Mahmood Yakubu lokacin da yake mika INEC. Hoto: INEC Nigeria
Source: Twitter

Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance, amma bayan tafiyar Farfesa Yakubu, ana sa ran kowane lokaci daga yanzu Tinubu na iya sanar da wanda ya zaba.

Jam'iyyu sun kawo mafita kan nadin shugaban INEC

A wani labarin, kun ji cewa jam'iyyun siyasa da ke da rajista karkashin inuwar Inter-Party Advisory Council (IPAC), sun ba da shawara kan nadin shugaban hukumar INEC.

Kara karanta wannan

Jam'iyyun siyasa sun cin ma matsaya kan nada sabon shugaban hukumar INEC

Sun nemi a kafa sabuwar hukuma mai zaman kanta wacce za ta riƙa naɗa shugaban INEC, kwamishinoni da sakatare na hukumar zaben Najeriya.

A cewarsu, tsarin yanzu da ake amfani da shi wanda shugaban kasa ke nada shugaban INEC, ya take 'yancin da hukumar ke da shi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262