Dalilin Gwamna Abba na Raba wa Matasa 5,384 Tallafin Naira Miliyan 807 a Kano

Dalilin Gwamna Abba na Raba wa Matasa 5,384 Tallafin Naira Miliyan 807 a Kano

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da rabon tallafin matasa a Kano, inda mutane 5,384 suka samu jarin N150,000 kowanne
  • An kawo shirin ne don tallafawa matasa wajen fara sana’o’in dogaro da kai, yayin da aka ba wasu kudin don fadada kasuwancinsu
  • Gwamna Abba ya ba da hakuri ga wadanda ba su samu damar da shiga cikin kashin farko na shirin ba, inda ya daukar masu alkawari

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da rabon N150,000 ga matasa a matsayin matakin farko na shirin KSYEP.

Shirin KSYEP dai an tsara shi domin baiwa matasa damar fara sana’o’i ko kuma faɗaɗa harkokin kasuwancinsu ta hanyar ba su tallafin kudi.

Gwamna Abba Yusuf ya kaddamar da shirin tallafawa matasan Kano da N150,000
Gwamna Abba Yusuf na daga hannu ga dubunnan matasan da ya ba tallafin N800m a Kano. Hoto: @Kyusufabba
Source: Twitter

Abba ya rabawa matasa N150,000 a Kano

Kara karanta wannan

Siyasar Najeriya: Zuwa kotu da abubuwan da ake fada kan takarar Jonathan a 2027

A sanarwar da ya fitar a shafisa na X, Gwamna Abba ya sanar da cewa matasa 5,384 - maza da mata ne suka amfana da kashin farko na shirin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce an raba wa kowanne matashi N150,000 domin gina kasuwanci ko kuma fadada kasuwancin da yake yi a lokacin.

Gwamna Abba Yusuf ya ce:

"A yau, mun dauki wani babban mataki na bunkasa matasanmu ta hanyar kaddamar da kashin farko na shirin tallafawa matasan Kano (KSYEP).
"An samar da wannan shirin ne domin tallafawa matasanmu da ke harkokin kasuwanci ta hanyar ba su kudin fadada kasuwancin, da wadanda ke farawa yanzu.
"A wajen taron, na bayyana cewa matasa 5,384, maza da mata ne suka samu tallafin N150,000 kowannensu."

Dalilin Abba na tallafawa matasa da N150,000

Rahoto ya nuna cewa an kaddamar da shirin ne a ranar Talata a Kano, a wani bangare na kokarin gwamnatin Abba na magance matsalar rashin ayyuka da koma sa matasa su dogara da kansu.

Gwamna Abba ya ce an samar da shirin don bunkasa matasa da jarin da suke bukata, wanda zai sanya su zamo daga cikin masu gina tattalin Kano.

Kara karanta wannan

Abba ya jero bangarori 5 da gwamnatin Kano ta farfado da su a cikin shekaru 2

"Wannan shirin zai taimakawa matasanmu su zamo daga cikin 'yan jihar da ke harkokin kasuwanci, wanda zai taimaka wajen ci gaban al'umma."

- Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Gwamna Abba ya ce manufar shirin ba da tallafin shi ne bunkasa matasan Kano kan harkokin kasuwanci.
Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf zaune a dakin taron kaddamar da tallafawa matasa sama da 5,000. Hoto: @Kyusufabba
Source: Twitter

Gwamna ya yi magana da matasan Kano

Ya bukaci wadanda suka samu tallafin da su yi amfani da tallafin kudin yadda ya kamata don faɗaɗa sana’o’insu da kuma gina kyakkyawar makoma.

Haka kuma, gwamnan ya roƙi waɗanda ke cikin jerin jiran tallafi na gaba da su yi hakuri, yana mai tabbatar da cewa za a yi rabon tallafin kashi na biyu nan ba da jimawa ba.

Gwamna Abba ya kuma ba da tabbacin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da shirye-shirye da tsare-tsare da za su fifita ci gaban matasa, samar da ayyuka da walwalar jama'ar Kano.

Gwamna zai nada sababbin kwamishinoni

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aika da sunayen wasu mutane ga majalisar dokoki don nada su kwamishinoni.

Abba Kabir Yusuf ya mika sunayen ne ga majalisar domin tantancewa da tabbatarwa a matsayin kwamishinoni kuma mambobin majalisar zartarwa.

Kara karanta wannan

Kwamishinan 'yan sanda ya fusata Gwamna Abba a wurin faretin ranar 'yancin kai a Kano

Mutanen biyu suna da kwarewa a fannonin da su ke aiki, kuma sun fito ne daga kananan hukumomin Bichi da Minjibir kamar yadda rahoto ya nuna.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com