Asiri Ya Tonu: Dakarun Sojoji Sun Cafke Masu Hada Baki da 'Yan Ta'adda a Katsina

Asiri Ya Tonu: Dakarun Sojoji Sun Cafke Masu Hada Baki da 'Yan Ta'adda a Katsina

  • Dubun wasu masu hada baki da 'yan ta'adda ta cika bayan sun fada komar jami'an tsaro a jihar Katsina
  • Dakarun sojoji tare da hadin gwiwar jami'an rundunar C-Watch sun samu nasarar cafke mutanen da ake zargi bayan gudanar da bincike
  • Hakazalika, sojojin sun kuma samu nasarar ceto wani mutum da 'yan ta'adda suka dauke yana tsaka da aiki a gonarsa

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Katsina - Dakarun sojojin Najeriya na rundunar Operation Fansan Yanma tare da haɗin gwiwar jami'an rundunar C-Watch, sun cafke wasu mutane a Katsina.

Dakarun sojojin sun kama mutanen ne bisa zargin hada baki da ‘yan ta’adda a karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina.

Sojoji sun cafke mutanen da ake zargi a Katsina
Shugaban sojojin kasa, Laftanar Olufemi Oluyede da gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda Hoto: @HQNigerianArmy, @dikko_radda
Source: Twitter

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai kazamin hari, an rasa rayukan jami'an tsaro a Kwara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun cafke masu hada baki da 'yan ta'adda

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa waɗanda aka kama sun haɗa da mai samar da kayan aiki, Aminu Rabiu Zango, mai shekara 52, da kuma wani mai ba ‘yan ta’adda bayanai, Alhaji Abdulrahman Tambaya, mai shekara 52.

"Aminu Rabiu Zango ya amsa cewa ɗansa ne ke kai wa shugaban ‘yan ta’adda Babaru makamai da alburusai, kuma kwanan nan ya koma Karu a Abuja."
"Haka kuma ya amsa cewa yana aiki ne karkashin Alhaji Iliya Zango, wanda ake cewa shi ne na gaba da Babaru."
"Alhaji Abdulrahman Tambaya kuma an same shi da ɗaya daga cikin lambobin wayar da Babaru ke amfani da su a wayarsa."

- Wata majiya

Majiyar ta kara da cewa wani da ake zargin yana samar da kayan aiki, Ado Dan Zaria, ya tsere ta hanyar tsallaka katangar gidansa lokacin da sojoji suka iso.

Jami'an tsaro sun gudanar da bincike a gidansa sannan daga bisani aka rushe shi.

Kara karanta wannan

Bulama Bukarti ya hango matsaloli a sulhu da ƴan ta'adda, ya ba gwamnati shawara

Sojoji sun ceto mutumin da aka sace

Haka kuma, dakarun sojojin sun ceto wani mutum da aka sace a karamar hukumar Kankara.

Mutumin da aka ceto mai suna Mallam Yakubu Abdullahi, mai shekara 55, yana sana'ar sayar da shayi.

Sojoji sun cafke masu hada baki da 'yan ta'adda a Katsina
Taswirar jihar Katsina, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

An samu nasarar ceto shi ne a tsaunukan Zango bayan ya tsere daga hannun ‘yan ta’adda.

"An sace shi ne a ranar 27 ga Satumba tare da wasu mutane biyu a gonarsu da ke hanyar Bagoma a Kankara. Ya samu damar tserewa yayin da ‘yan ta’addan suka gudu cikin duwatsu tare da sauran mutanen da suka sace."

- Wata majiya

Majiyar ta kara da cewa an tantance bayanan wanda aka ceto, kuma nan ba da jimawa ba za a haɗa shi da iyalansa.

Jami'an tsaro sun dakile harin 'yan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa jami'an tsaro sun samu nasarar dakile wani harin da 'yan bindiga suka kai a jihar Katsina.

Kara karanta wannan

An kama dilolin makamai a Nijar, an fara binciken 'yan siyasar Najeriya

'Yan bindigan sun kai harin ne a karamar hukumar Danja, inda suka yi yunkurin yin garkuwa da wasu mutane.

Sai dai, jami'an tsaro sun yi artabu da su, inda suka samu nasarar hallaka daya daga cikinsu tare da kubutar da mutanen da suka yi yunkurin sacewa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng