Girma Ya Fadi: Basarake Ya Rasa Sarauta kan Zargin Satar Tiransifoma 2

Girma Ya Fadi: Basarake Ya Rasa Sarauta kan Zargin Satar Tiransifoma 2

  • Wani mai rike sarautar gargajiya ya rasa kujerarsa bayan zarginsa da satar injunan wutar lantarki a jihar Osun
  • Oba Clement Adesuyi Haastrup Ajimoko III, Owa Obokun na Ijesa, ya tsige Busuyi Gbadamosi, bisa zargin da ake yi masa
  • An ce shugaban ya kasa maido da injunan duk da umarnin fada da shawarwarin kwamitin sasanta rigingimun sarauta

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Ilesa, Osun - Rundunar yan sanda a jihar Osun ta tabbatar da kama basarake kan zargin satar injunan wutar lantarki.

Oba Clement Adesuyi Haastrup Ajimoko III, Owa Obokun na Ijesa, ya tsige daya daga cikin masu sarautar gargajiya, Busuyi Gbadamosi, bisa zargin satar injunan wutar lantarki guda biyu na al’umma.

An tube basarake kan zargin satar transifoma
Sarkin Ijesa, Oba Clement Adesuyi Haastrup da wanda ake zargi, Busuyi Gbadamosi. Hoto: Issac Haastrup.
Source: Facebook

Hakan na cikin wata sanarwa da dan gidan sarautar Ijesa, Isaac Haastrup wanda kuma dan jarida ne ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Babban Sarki ya rasu a Najeriya, Sarkin Musulmi ya taka har fada yin ta'aziyya

Zargin da ake yi wa basaraken a Osun

Sarkin ya bayyana cewa an dauke injunan masu karfin 300KVA da 500KVA ne a shekarar 2023 lokacin mulkin marigayi Oba Gabriel Adekunle Aromolaran.

Shugabannin al’umma sun tabbatar da cewa Gbadamosi ya cire injunan da dare, sannan ya yi ƙoƙarin rufe laifinsa ta hanyar ba da kuɗi.

Lokacin bincike, Gbadamosi ya amsa cewa ya sayar da injin mai karfin 300KVA kan N120,000 kuma ya kai ɗayan Ibadan wai domin gyara.

Duk da bai cika wa’adin kwanaki 30 da aka ba shi ba, da ƙarin kwanaki bakwai, Oba ya tsige shi daga matsayin Oba-Odo na Ilesa.

Oba ya umarci jama’a su guji kiransa da suna Oba-Odo, tare da barin gidan sarauta, domin kare darajar masarautar Ijesa.

Biyo bayan ƙin bin umarni, Owa Obokun ya ƙara wa Gbadamosi kwanaki bakwai. Amma da bai cika wa’adin ba, Sarki ya umarci tsige shi daga mukamin sa.

Kara karanta wannan

Sarki ya kinkimo bukatar kirkiro jiha 1, ya fadawa Tinubu gaba da gaba a Ibadan

Sanarwar ta ce:

“Daga yau, Chif Busuyi Gbadamosi ba za a sake kiransa da Oba-Odo na Ilesa ba, ya gaggauta barin gidan sarauta da ke kulle.”
An sauke basarake daga mukaminsa kan zargin sata a Osun
Taswirar jihar Osun da ke Kudu maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Gargadin da aka yiwa jama'a kan basaraken

An sanar da jama’a cewa ka da su sake kiran ko mu’amala da shi a matsayin Oba-Odo, Sarkin ya ce an ɗauki matakin kare al’adar Ijesa ne.

Mutane da dama sun yi ta magana kan dalilin tube shi ba tare da kammala bincike ba inda suke ganin ya kamata a ba shi dama domin kare kansa game da zargin.

Rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta tabbatar da kama shi kan zargin satar injunan, inda aka ce bincike kan lamarin yana ci gaba da gudana.

Ana zargin kansila, basarake da satar transifoma

A wani labarin, dubun wasu manya a cikin al'umma ta cika bayan cafke su da zargin satar tiransifomar wutar lantarki a jihar Gombe.

Kara karanta wannan

Magana ta kare, tsohon gwamna ya zama Sarki mai martaba a Najeriya

Rundunar ƴan sanda ta yi nasarar cafke kansila da kuma dagacin kauyensu kan zargin sata da kuma siyar da tiransifoma.

Kakakin rudunar 'yan sanda a Gombe, ASP Buhari Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin da halin da ake ciki bayan zarginsu da almundahana.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com