Dama Ta Samu: Gwamna Zai ba Malaman Sakandare Rancen N569m Su Sayi Mota da Gida

Dama Ta Samu: Gwamna Zai ba Malaman Sakandare Rancen N569m Su Sayi Mota da Gida

  • Gwamna Biodun Oyebanji ya amince da bayar da rancen N596.6m ga malamai da ma’aikatan makarantun sakandare a Ekiti
  • Babban sakataren hukumar kula da malaman sakandare, Michael Boluwade, ya ce rancen kudin na sayen motoci da gidaje ne
  • A gefe guda, Gwamna Oyebanji ya riga ya amince da sakin N200m a matsayin rancen sayen gidaje da motoci ga malaman firamaren jihar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Ekiti - Malaman makarantun sakandare na cikin alheri dumu-dumu yayin da gwamnan Ekiti ya amince a ba su rancen Naira miliyan 596.6.

Gwamna Biodun Oyebanji ya amince a ba malamai da ma'aikatan da ba malamai ba, su 807 rancen kudin don su sayi motoci da gidaje.

Gwamnan Ekiti ya amince a ba malaman sakandare rancen Naira miliyan 596.6 domin su sayi motoci da gidaje
Gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji yana jawabi a taron majalisar EoDB a ofishinsa da ke Ado Ekiti. Hoto: @biodunaoyebanji
Source: Twitter

Ekiti: Za a ba malamai rancen N596.6m

Babban sakataren hukumar kula da malamai ta jihar Ekiti, Michael Boluwade ne ya sanar da hakan a sanarwar da ya fitar ranar Talata a Ado Ekiti, inji rahoton Punch.

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: NLC ta taso gwamna a gaba, tana so ya kara albashi zuwa N256,960

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar Michael Boluwade, ba da rancen kudin na daga cikin kokarin Gwamna Oyebanji na inganta walwalar malaman sakandare da firamare na gwamnati.

Sanarwar ta ce:

"Daga cikin kudin da aka amince a raba, an ware N381.5m domin ba mutane 382 rance don su sayi motoci, sannan an ba mutane 425 rancen N215.1m don su sayi gidaje.
"Za a raba wannan kudin ga malamai da ma'aikatan da ba malamai ba da ke aiki a makarantun sakandare, bisa ga umarnin gwamna na karin da aka samu."

Babban sakataren ya jinjinawa Gwamna Oyebanji bisa amincewa da fitar da kudin ga asusun ba da lamuni na hukumar, wanda zai sa a rabawa masu cin gajiya da wuri.

Gwamna ya fara cika alkawari ga ma'aikata

Ya shawarci wadanda za su amfana da rancen da su yi amfani da kudin bisa ga abin da suka nema, yana mai tunatar a su cewa za su biya bashin ne ta hanyar cire wani bangare na albashinsu.

Kara karanta wannan

Sabuwar cuta mai cin naman jiki ta bulla a Adamawa, gwamnati ta fara bincike

Idan za a iya tunawa, Gwamna Oyebanji, a ranar ma'aikata ta 2025, ya ce gwamantinsa ta kaddamar da shirye-shiryen da za su inganta walwalar ma'aikata.

Ya lissafa shirye-shiryen da suka had ada ba da rancen N400m na sayen motoci da gidaje ga malamai da ma'aikatan da ba malamai ba, har su 1447.

Gwamnan Ekiti ya riga ya amince a ba malaman firamare rancen N200m don su sayi gidaje da motoci
Taswirar jihar Ekiti da ke a Kudancin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Wannan na zuwa ne yayin da Gwamna Oyebanji, ya amince da sakin N200m domin ba da rancen sayen motoci da gidaje ga malaman firamare a jihar.

Wannan mataki ya cika alkawarin gwamnan na tabbatar da cewa malaman firamare na gwamnati sun fara cin moriyar wasu shirye-shirye da takwarorinsu dake koyarwa a makarantun sakandare ke ci.

Wata sanarwa da aka wallafa shafin gwamnatin Ekiti na intanet ya nuna cewa an riga an tura N50m zuwa asusun masu cin gajiyar shirin a Janairu, bisa ga umarnin gwamnan.

Ekiti: Gwamna ya ba ma'aikata kyautar N42m

A wani labarin, mun ruwaito cewa, gwamnan Ekiti, Biodun Oyebanji ya yaba da kokarin wasu ma’aikata 82 ta hanyar ba su kyautar tsabar kudi har N42m

A yayin wani taron kungiyar ma’aikatan gwamnati, Oyebanji ya yi wa ma’aikatan Ekiti alkawari kan inganta walwalarsu tare da ci gaba da biyan sabon albashi.

Kara karanta wannan

TIN: Muhimman abubuwa 11 game da sabuwar lambar haraji da za ta fara aiki a 2026

Gwamnan ya kuma yaba wa ma’aikatan bisa hakurin da suka nuna, ya yi alkawarin cewa nan ba da dadewa za su kara shan romon dimokuradiyya daga gwamnatinsa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com