Za Ayi Nasara, Gwamna Dikko Radda Ya Fadi Babbar Hanyar Kawo Karshen Ta'addanci

Za Ayi Nasara, Gwamna Dikko Radda Ya Fadi Babbar Hanyar Kawo Karshen Ta'addanci

  • Gwamna Dikko Radda ya bayyana cewa ingantaccen ilimi na daya daga cikin manyan hanyoyin magance matsalolin tsaro a Arewa
  • Gwamnan na Katsina, ya ce gwamnatinsa ta zuba jari mai yawa a fannin ilimi, ciki har da tallafa wa ƙungiyoyin da ke habaka ilimi
  • Ya ce gwamnatinsa ta kaddamar da makarantu na musamman uku, yayin da dalibai da dama ke samun tallafin karatu a ƙasashen waje

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Katsina - Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa ilimi shi ne ɗaya daga cikin manyan makamai na yaki da rashin tsaro.

A cewar Gwamna Dikko Radda, da ilimi ne za a magance matsalar rashin tsaro daga tushe, kamar dai ace a tuge jijiyar bishiya don kashe ta gaba daya.

Gwamna Dikko Radda ya ce ilimi na taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar tsaro.
Gwamnan jiyar Katsina, Gwamna Dikko Umar Radda yana aiki a ofishinsa. Hoto: @dikko_radda
Source: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Hanyar magance matsalar tsaro' - Gwamna Radda

Kara karanta wannan

Gwamnan Bauchi ya kori malamin makaranta daga aiki bayan ya aikata babban laifi

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, gwamnan na Katsina ya ce:

“Ilimi mai inganci na taka muhimmiyar rawa wajen yaki da rashin tsaro ta hanyar rage talauci, jahilci da rashin aikin yi.
"Yana bai wa mutane kwarewa da basira da dabi’u masu kyau domin samar da tunani mai zurfi, haƙuri da ɗabi’ar zama ɗan ƙasa nagari.”

Ya ƙara da cewa al'ummar da ta samu ingantaccen ilimi na iya guje wa yaudarar miyagun mutane, tsattsauran ra’ayi da tashin hankali.

Haka kuma, ilimi na taimakawa wajen ƙarfafa haɗin kai a cikin al’umma, bunƙasa tattalin arziki da kuma gina ƙwararrun cibiyoyin gwamnati da ake buƙata domin dorewar zaman lafiya da tsaro.

Gwamna Radda ya saka hannun jari a ilimi

Gwamna Dikko Radda ya bayyana cewa gwamnatin sa na ci gaba da zuba jari a fannin ilimi ta hanyoyi daban-daban.

Ya ce gwamnati na tallafawa shirye-shiryen ƙungiyoyi masu zaman kansu da ke taimakawa wajen ƙara samun damar karatu, musamman a yankunan karkara.

Kara karanta wannan

"Ina kan bakata," Abba Gida Gida ya yi maganar yadda ya tsira da kujerarsa

Gwamnan ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da Dan Amana Tested and Trusted Initiative a Katsina, inda ya jaddada cewa manufar gwamnatin sa ita ce “Gina makomarka ta hanyar ilimi."

Ya kuma bayyana cewa tun farkon mulkinsa gwamnatin ta tura yara daga Katsina zuwa kasashen waje domin karatu a fannonin da ake buƙata.

“Mun tura yara karatu a fannin likitanci a Misira da kirkirarriyar fasa ta AI a China bisa cancanta. Ina alfahari da cewa suna yin fice a fannoni daban-daban,” in ji Dikko Radda.
Gwamna Dikko Radda ya ce gwamnatinsa ta dauki yaran Katsina ta tura su kasashen waje yin karatu mai zurfi.
Gwamnan Katsina a wajen kaddamar da wani shiri kan ilimi. Hoto: @dikko_radda
Source: Twitter

Shirye-shiryen makarantu na musamman

Radda ya sanar da kafa shirin Makarantu na Musamman a Katsina, wanda ya haɗa da gina makarantu na zamani a Radda, Jikamshi da Dumurkul.

Ya ce makarantun za su zama cibiyoyin gano yara masu kaifin basira a Katsina, kuma za a dauki dalibai da malamai bisa cancanta kadai, ba tare da la’akari da asalinsu ko matsayinsu na zamantakewa ba.

A cewar gwamnan, waɗannan tsare-tsare na nuna jajircewar gwamnatin Katsina wajen ɗaga matsayin ilimi, karfafa nagarta da samar da ci gaban da zai dore a jihar.

Gwamna Dikko Radda ya lashe zambar yabo

Kara karanta wannan

Sabon tarihi: Dubban 'yan auren jinsi sun gudanar da ziyarar bauta a Vatican a karon farko

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Raɗɗa ya lashe lambar yabo ta gwamnan da ya fi kowane aiki a shekarar 2025.

Kamfanin Aso Multimedia ne ya ba Gwamna Radda wannan lambar yabo domin yabawa kokarin da yake wajen kawo ci gaba a jihar Katsina.

Kwamishinar harkokin mata ta Katsina, Hajiya Hadiza Yar’adua ta faɗi wasu daga cikin ayyukan da Dikko Raɗɗa ya yi a shekaru biyu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com