A Karshe, Kotun Abuja Ta Yanke Hukunci kan Shugaban Kungiyar Ansaru da Aka Cafke

A Karshe, Kotun Abuja Ta Yanke Hukunci kan Shugaban Kungiyar Ansaru da Aka Cafke

  • Wata Kotu da ke zamanta a birnin Abuja ta yanke hukunci kan wasu daga cikin kwamandojin kungiyar Ansaru da aka kama kwanakin baya
  • Kotun ta yanke wa Mahmud Usman, kwamandan Ansaru, hukuncin shekaru 15 bayan ya amsa laifin ma’adinai ba bisa ka’ida ba
  • Mai shari’a Emeka Nwite ya ba da umarnin a tsare shi har zuwa shari’ar sauran tuhume-tuhume 31, inda aka dage zuwa Oktoba 21

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Alhamis ta yi zama domin yanke hukunci kan kwamandan kungiyar Ansaru.

Kotun ta yanke wa kwamandan, Mahmud Usman, hukuncin daurin shekaru 15 a gidan gyaran hali bayan samun shi da laifuffuka da suka shafi ta'addanci.

An yanke wa kwamandan Ansaru hukunci bayan Ribadu ya tabbatar da kama shi
Hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa da Malam Nuhu Ribadu. Hoto: HQ Nigerian Army, Nuhu Ribadu
Source: Facebook

An gurfanar da 'dan kungiyar Ansaru a kotu

Rahoton Channels TV ta ce hukuncin ya biyo bayan cafke wasu daga cikin kwamandojin Ansaru wanda Usman na cikinsu.

Kara karanta wannan

Sanata Ndume ya 'gano' makircin masu kiran a kori hafsoshin tsaro, ya gargadi Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar DSS ce ta gurfanar Usman, wanda ya amsa laifin hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba da aka ce ya taimaka masa wajen samun makamai don ta’addanci da satar mutane.

Mai shari’a Emeka Nwite ya ba da umarnin a tsare shi a hannun DSS har zuwa shari’ar sauran tuhume-tuhume 31 da ake masa.

Wace tuhuma ake yi wa 'dan Ansarun?

A cikin tuhume-tuhume 32, an zargi Usman da Abubakar Abba da kai hari Wawa Cantonment na Sojojin Najeriya a Kainji, Niger a 2022.

An ce harin ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, tare da samun horo kan makamai da kera abubuwan fashewa daga sansanonin ta’addanci daban-daban.

Haka kuma, an ce sun samu horo kan dabarun yaki daga wata ƙungiyar ta’addanci a Mali, kafin kotu ta dage shari’a zuwa Oktoba 21.

DSS ta zargi shugabannin da kitsa harin gidan yarin Kuje a 2022, wanda ya kubutar da sama da fursunoni 600 a lokacin.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu zai yi jawabi kai tsaye ga 'yan Najeriya

Kotu ta daure shugaban kungiyar Ansaru a gidan kaso
Malam Nuhu Ribadu da shugaban kungiyar Ansaru, Mahmuda Usman. Hoto: Federal Ministry of Information and Orientation, Nuhu Ribadu.
Source: Facebook

Sauran zarge-zarge da ake yi ga Ansaru

An kuma ce sun shirya kai hari kan wurin hakar ma'adinan uranium a Niger da garkuwa da Faranshi Francis Collomp a 2013, da sauran manyan laifuffuka, cewar rahoton Punch.

Nuhu Ribadu ya tabbatar da kama su, yana mai cewa an samu nasarar hakan ne bayan hadin gwiwar jami’an tsaro, inda ya bayyana Usman a matsayin jagoran Ansaru.

Ya ce Mamuda ya kasance yana jagorantar “dakin da ake kulle mutane da ake kira "Mahmudawa” a kusa da Kainji National Park, yayin da Ansaru ta samo asali a Kano a 2012.

Jami'an tsaro sun damke 'Yan Ansaru

A makonnin baya ne rahoto ya gabata cewa Gwamnatin Najeriya ta sha yabo bayan kama shugabannin 'yan kungiyar ta'addan Ansaru a kasar.

Amurka ta yaba da nasarar tare da kara karfafa jami'an tsaron Najeriya ganin wannan gagarumar nasara da aka samu a yaki da ta'addanci.

Kara karanta wannan

Hukumar EFCC ta gurfanar da 'yar takarar PDP a kotu kan zargin sabawa doka

Haka zalika Birtaniya ta yaba da kokarin mai ba shugaban kasa shawara a kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu wajen kama 'yan ta'addan.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.