Mamakon Ruwan Sama da Zai Sauka Ranar Talata Zai Jawo Ambaliya a Jihohin Arewa 2
- Hukumar NiMet ta yi hasashen cewa za a samu ruwan sama tare da iska mai karfi a jihohin Arewa, a ranar Talata, 9 ga Satumba, 2025
- NiMet ta ce ruwan sama kamar da bakin kwarya da zai sauka zai iya jawo ambaliya a wasu jihohin Arewa ta Tsakiya kamar Neja da Kogi
- A Kudu, jihohin Lagos, Ogun, Edo, Cross River da Akwa Ibom za su fuskanci ruwan sama mai yawa, wanda zai iya haddasa ambaliya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja – Hukumar da ke kula da hasashen yanayi ta kasa (NiMet) ta fitar da hasashen yanayi na ranar Talata, 9 ga watan Satumba, 2025.
Hasashen hukumar ya nuna cewa za a samu ruwan sama mai yawa, wanda zai sauka hade da iska mai karfi da tsawa, kuma zai jawo ambaliya a sassan kasar.

Kara karanta wannan
'Talauci ya yi muni a Najeriya,' El Rufa'i ya ce akwai mafita kan matsin tattalin arziki

Source: Original
Hukumar NiMet ta wallafa rahoton hasashen a shafinta na X a daren ranar Litinin, tana mai yin gargadi ga mazauna garuruwan da ke bakin koguna.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hasashen ruwan sama a yankin Arewa
NiMet ta bayyana cewa za a samu ruwan sama a safiyar Talata, a jihohin Taraba, Adamawa, Kebbi, Zamfara, Gombe, Bauchi, Kaduna, Sokoto da Katsina.
Hukumar ta ce a jihohin Borno, Sokoto, Kebbi, Bauchi, Kaduna, Adamawa, Jigawa, Kano, Katsina, Zamfara da Taraba za su sake samun ruwan sama mai yawa a yammacin Talata.
Wannan mamakon ruwan sama da za a yini ana yi, zai iya jawo tsaiko ga matafiya, yayin da iska da ruwa mai karfi ka iya jawo hadurran ababen hawa.
Hasashen ruwan a sauran jihohin Arewa
A yankin Arewa ta Tsakiya kuwa, hasashen ya nuna cewa za a samu ruwan sama mai sauƙi a wasu sassan Abuja, Kwara, Benue, Neja da Kogi tun daga safe.
A yammacin ranar kuwa, ruwan sama mai matsakaicin ƙarfi zai sauka a Nasarawa, Neja, Filato, Kogi, Kwara, Benue da Abuja.
NiMet ta yi gargadin cewa akwai yiwuwar a samu ambaliyar ruwa musamman a Neja da Kogi, inda ruwa ya cika tafkuna da manyan kogunan yankin.
Hasashen yanayi a Kudancin Najeriya
A kudancin Najeriya, NiMet ta ce za a fara da yayyafi a Ebonyi, Imo, Abia, Oyo, Ogun, Edo, Legas, Cross River da Akwa Ibom a safiyar Talata.
Daga baya kuma, ruwan sama mai karfi zai sauka a yawancin ranar a kusan dukkanin jihohin Kudancin kasar.

Source: UGC
Shawarar hukumar NiMet ga 'yan Najeriya
NiMet ta shawarci jama’a da su kasance cikin shiri, musamman masu zirga-zirga a manyan tituna saboda iska mai ƙarfi na iya rage gani da janyo hadurra.
Hakanan, hukumar ta bukaci al’ummar da ke rayuwa a wuraren da ke da koguna musamman a Neja da Kogi da su dauki matakan kariya daga hadarin ambaliya.
An samu mummunar ambaliya a Taraba
A wani labarin, mun ruwaito cewa, akalla garuruwa bakwai ne suka nutse a cikin ruwa, bayan afkuwar wata mummunar ambaliya a jihar Taraba.

Kara karanta wannan
Najeriya, ƙasashe 9 za su fuskanci kusufin wata, an ji tsawon lokacin da zai dauka
Kauyukan da ambaliyar ta shafa sun hada da garin Kunini a karamar hukumar Lau, inda ta rusa gidaje, ta lalata gonaki kuma ta hallaka dabbobi.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta NEMA ta sanar da cewa SEMA a Taraba ta kwashe wasu mazauna Lau da Jalingo zuwa wuri mai aminci.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
