Hatsarin Jirgi Ya Rutsa da Mutane kusan 100 a Hanyar zuwa Gidan Gaisuwa, An Rasa Rayuka

Hatsarin Jirgi Ya Rutsa da Mutane kusan 100 a Hanyar zuwa Gidan Gaisuwa, An Rasa Rayuka

  • Hukumar NSEMA ta tabbatar sa faruwar wani hatsarin jirgin ruwa a yankin karamar hukumar Borgu ta jihar Neja
  • Jirgin na dauke da mutane kusan 100, wanda aka gano cewa su na hanyar zuwa gaisuwar wata rasuwa da aka yi ne a yankin
  • Shugaban NSEMA, Abdullahi Baba Arah ya ce wadanda ke cikin jirgin sun karya dokar da gwamnatin Neja ta sanya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Niger - Rahotanni sun tabbatar da cewa an kara samun hatsarin jirgin ruwa da ya hallaka gomman mutane a yankin karamar hukumar Borgu ta jihar Neja.

Hatsarin jirgin ruwan, wanda ya dauko mutane kusan 100, ya yi sanadiyyar mutuwar fasinjoji 29, yayin da har yanzu ba a ga mutane biyu daga ciki ba.

Jirgin ruwa ya nutse a Niger.
Hoton wani jirgin ruwa da ya yi hatsari Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Jaridar Leadership ta tattaro cewa jami'an ceto da sauran mutanen da suka kai dauki sun samu nasarar ceto mutum 50 da da ransu a hatsarin wanda ya auku a Borgu.

Kara karanta wannan

Dakarun sojoji sun samu nasara kan 'yan bindiga bayan an yi gumurzu a Katsina

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda jirgin ruwa ya nutse da mutane 90

Bayanai sun nuna cewa hatsarin ya faru ne a kauyen Gausawa, da ke yankin Malale, inda aka tabbatar cewa mutum 90 ne ke cikin jirgin lokacin da hatsarin ya auku.

An gano cewa jirgin ya tashi ne daga Tugan Sule da ke cikin gundumar Shagunu, dauke da fasinjoji mafi yawansu mata da yara, da nufin zuwa Dugga domin yin gaisuwar rasuwa.

Wani ganau ya bayyana cewa jirgin ya cika makil da fasinjoji tun daga lokacin da ya bar Tugan Sule, sai da ya kusa isa Gausawa, sannan ya kife nan take.

Me ya haddasa hatsarin jirgin a Neja?

Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Abdullahi Baba ya ce:

“Mun samu rahoton hatsarin jirgin ruwa a wani kauye mai suna Gausawa da ke yankin Malale a karamar hukumar Borgu.

Kara karanta wannan

Masu garkuwa sun sato bala'i a Kano, wanda suka kama ya tona musu asiri

“Bisa ga rahoton jami’inmu da ke jagorantar aikin bincike da ceto, jirgin ya tashi daga garin Tugan Sule da fasinjoji 90 ciki har da mata da yara, inda suka nufi Dugga don yin gaisuwar rasuwa.”

Shugaban NSEMA ya bayyana cewa dalilan hatsarin sun haɗa da cika jirgin fiye da kima da kuma bugun wata bishiya da ke ƙarƙashin ruwa.

Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Niger.
Hotom gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago a fadar gwamnatinsa da ke Minna Hoto: @HonBago
Source: Twitter

NSEMA ta tabbatar da ceto mutane 50 a raye

Haka kuma, ya tabbatar cewa babu wanda ya sanya rigar ruwa saga cikin fasinjojin jirgin duk da dokar gwamnati da ta tilasta hakan a jihar, in ji Punch.

Ya ƙara da cewa, an riga an ceto mutane 50 da ransu, sannan an ciro gawarwakin mutum 29, yayin da ake cigaba da aikin bincike don gano sauran mutum biyu da suka ɓace.

Jirgin ruwa ya nutse da mutane a Sakkwato

A wani labarin, kun ji cewa jirgin ruwa dauke da mutane da dama ya kife a yankin karamar hukumar Shagari ta jihar Sakkwato.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jirgin ruwan wanda ke cike da fasinjoji har ya wuce kima, ya nutse a ruwa lamarin da ya jawo asarar rayuka da kuma bacewar wasu.

Wasu shaidu sun ce jirgin da ya yi hatsarin ya dauko maza, mata da yara fiye da ƙima kafin kifewarsa a tsakiyar ruwa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262