'Adawa da Gwamna': Ƴan Daba Sun Zare Wuƙaƙe, Sun Tarwatsa Taron Tsaro a Katsina

'Adawa da Gwamna': Ƴan Daba Sun Zare Wuƙaƙe, Sun Tarwatsa Taron Tsaro a Katsina

  • Taron tsaro da kungiyar KSCI ta shirya ya gamu da cikas bayan wasu da ake zargi da ’yan daba ne suka farmaki mutane da wukake
  • Rikicin ya tashi ne bayan Dr Bashir Kurfi ya bayyana yadda ’yan bindiga suka mamaye garuruwa da makarantu a jihar Katsina
  • 'Yan daban sun kai hari kan ’yan jarida, wasu ma sun fito da makamai, yayin da suka ce ba za su bari a soki gwamnatin Dikko Radda ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Katsina – Wasu da ake zargi da ’yan daba ne sun tarwatsa wani taron tsaro a jihar Katsina a ranar Talata, tare da kai hari ga mahalarta taron da ma ’yan jarida.

Taron, wanda kungiyar ci gaban tsaron Katsina (KSCI) ta shirya, ya haɗa masana tsaro, jami’an soja da ’yan sanda da suka yi ritaya, da malamai, da shugabanni, don tattaunawa kan matsalar tsaron jihar.

Kara karanta wannan

An kama tarin makamai ana kokarin shiga da su Katsina daga Jigawa

'Yan daba sun tarwatsa taron tsaro da aka shirya a Katsina
Taswirar jihar Katsina da ke a shiyyar Arewa maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Katsina: 'Yan daba sun hargitsa taron tsaro

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, an fara taron cikin lumana, har zuwa lokacin da Dr Bashir Kurfi, wanda ya shirya taron ya fara jawabi kan halin da jihar ke ciki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dr. Bashir ya bayyana cewa hare-haren 'yan bindiga ya ruguza wasu kananan hukumomi a Katsina, inda harkokin noma da kiwo suka tsaya cak, kuma an rufe makarantu, ko kuma ’yan bindigar sun mamaye su.

Sai wani mutum ya katse maganarsa da cewar gwamnati na bakin kokarinta, kuma bai amince a ci gaba da abin da ya kira 'suka da adawa ga gwamnati' ba.

Katsina: Hankula sun tashi a taron tsaro

Bayan haka, wasu da dama daga cikin wadanda ake zargin 'yan daba ne suka tashi suka fara hayaniya, suna yin wurgi da kujeru tare da kai hari ga ’yan jarida.

Shaidun gani da ido sun ce wasu daga cikin mutanen da suka hargitsa taron sun fito da wukake, suna barazanar farmakar duk wanda ya zama “makiyi ga gwamnati”.

Kara karanta wannan

'Ba ruwanmu,' ADC ta juya wa El Rufai baya kan taron da ya jawo rikici a Kaduna

Wani mahalarcin taron ya bayyana cewa, ’yan daba sun dade a wajen taron, a ciki da wajen wurin zama, suna jiran damar tada rikici.

Masu shirya taron sun mayar da martani

Daga bisani, Dr Kurfi da abokan aikinsa sun yi taron manema labarai a wani wurin daban, inda suka ce za su ci gaba da shirya taro kan yanayin tsaro a Katsina.

Sun ce abin mamaki ne ganin gwamnati ta yi irin wannan abu, duk da cewa an sanar da ita tun daga tarurrukan baya da aka yi a Abuja da Kaduna.

Dr Kurfi ya yi zargin cewa shugabannin kananan hukumomi na da hannu a hargitsin, yana mai cewa an ga daya daga cikinsu yana ba ’yan daba kudi.

Masu shirya taron sun zargi gwamnatin Katsina da sanya 'yan dabar su tarwatsa taron duk da sun sanar da ita shirinsu.
Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda a gidan gwamnati. Hoto: @dikko_radda
Source: Facebook

Martanin gwamnatin Katsina kan taron tsaro

Da aka tuntubi gwamnatin jihar Katsina, kwamishinan watsa labarai da al’adu, Dr Bala Salisu Zango, ya ce bai san da taron ba balle rikicin da ya faru.

Amma ba a samu amsar sakon da aka tura ga daraktan yada labarai na gwamna, Maiwada Dammallam ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Kara karanta wannan

'Yan daba sun tarwatsa taron ƴan adawa da El Rufa'i ya halarta a Kaduna, an ji raunuka

Radda, kusoshin Katsina sun gana da Tinubu

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya ba sojoji da sauran jami'an tsaro umarnin tsaurara sa ido kan hare-haren 'yan bindiga a Katsina.

Tinubu ya nuna takaicinsa kan yadda matsalar tsaro ke ci gaba da tabarbarewa a Katsina, yana mai cewa, za a sake fasalin yadda ake yakar 'yan ta'adda a jihar.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da wata tawaga daga jihar Katsina karkashin jagorancin Gwamna Dikko Umaru Radda, ta gana da shi a fadar shugaban kasa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com