An Kama Sojan Najeriya Ya Yi Lalata da Matar Abokin Aikinsa, An Yanke Masa Hukunci

An Kama Sojan Najeriya Ya Yi Lalata da Matar Abokin Aikinsa, An Yanke Masa Hukunci

  • Wata kotun soja ta musamman ta yanke wa wani Laftanal hukuncin shekaru uku a gidan yari tare da korarsa daga aikin sojan ruwa
  • An samu Laftanal din da laifin yin lalata da matar wani jami’in soja da kuma aikata ayyukan da suka sabawa dokar aiki
  • An rahoto cewa hukuncin ya fara aiki tun daga ranar 23 ga Nuwamba, 2024, kuma an aiwatar da shi a dandalin horo na NNIT, Sapele

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Rundunar sojan ruwa ta Najeriya (NN) ta kori wani jami’i mai mukamin Laftanal daga aiki tare da yanke masa hukuncin shekaru uku a gidan yari.

Rahoto ya bayyana cewa an yanke wa sojan wannan hukuncin ne bayan da aka same shi da laifin kulla alaƙar soyayya da matar wani soja, har ta kai su ga lalata.

Kara karanta wannan

MURIC ta kausasa harshe kan kisan matar da ake zargi da kalaman batanci a Neja

Kotun soja ta kori wani sojan ruwan Najeriya mai mukamin Laftanal saboda kama shi da laifin lalata da matar abokin aikinsa.
Rundunar sojin ruwa ta kori wani jami'inta daga aiki bisa zargin lalata da yarinya. Hoto: Naija_PR/X A kula, hoton ba shi da alaka da wannan labari, an sanya shi don misali kawai.
Source: UGC

An samu soja da laifuffuka 4

Kotun soja ta musamman (SCM) ce ta yanke hukuncin, bayan gudanar da shari’ar sojan bisa umarnin hedikwatar rundunar a Abuja, inji rahoton Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni sun tabbatar da cewa an gurfanar da jami’in bisa zargin aikata laifuffuka guda hudu, ciki har da yin lalata da matar soja, wanda ya sabawa sashi na 79 na dokar sojoji (AFA) CAP A20 LFN 2004.

Haka kuma, an tuhume shi da aikata abin kunya da bai dace da matsayin soja ba, wanda ya saba wa sashe na 91, da kuma yaudarar shaida har sau biyu, laifin da ya saba wa sashe na 122 na dokar ta'addanci (CCA), bisa ga sashin 114 na AFA.

An ba sojan damar kare kansa gaban kotu

Majiyoyi sun ce kotun sojin ta gudanar da shari’ar cikin adalci tare da ba jami’in damar kare kansa, daga farko har zuwa lokacin kammala shari’ar.

Kara karanta wannan

NDLEA ta kama tsoho mai shekara 70 da miyagun kwayoyi, an lalata gonar wiwi

Rahoton Pulse.ng ya nuna cewa an bi dukkan matakan da doka ta tanada kafin a yanke wa sojan hukuncin.

Daga karshe, an rahoto cewa rundunar sojan ruwa ta amince da hukuncin korar jami'in daga aiki tare da yanke masa hukuncin shekaru uku a gidan yari.

An tabbatar da cewa hukuncin da aka yanke wa sojan ruwan ya yi daidai da dokokin aikin soja
Taron sojojin ruwan Najeriya da aka kara wa matsayi zuwa Admirals a hedikwatar sojin ruwa da ke Abuja. Hoto: @NigerianNavy
Source: Twitter

Hukuncin ya yi daidai da dokar soja

Rundunar sojan ruwa ta bayyana cewa hukuncin ya yi daidai da sashi na 117(7) na dokar AFA, wanda ke umartar cewa za a kori jami’in da kotun soja ta yanke masa hukuncin zaman gidan yari.

An rahoto cewa hukuncin ya fara aiki tun daga ranar 23 ga Nuwamba, 2024, kuma an fara hukunta sojan a dandalin horo na cibiyar fasahar sojin ruwan Najeriya (NNIT), da ke Sapele, a ranar 29 ga Agusta, 2025.

A cewar majiyar tsaro, wannan hukunci na daga cikin matakan da rundunar ke ɗauka don tabbatar da ladabi, gaskiya da kuma kiyaye mutuncin sojoji yayin da suke aiki.

Soja ta ce manyan jami'ai na cin zarafinta

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wata soja ta fito ta zargi manyan jami'an sojojin Najeriya da azabtar da ita sabuwa ta ki yarda su yi lalata da ita.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Ɗan sanda ya saita bindiga, ya harbe soja har lahira a Bauchi

A cikin wani bidiyo da ta dauka, sojar ta ce an kore ta daga gidanta, an kuma kai ta asibitin masu tabin hankali duk don a ci zarafinta.

Ba iya nan ta tsaya ba, sojar ta ce kin amincewa da bukatar shugabanninta na yin lalata da ya sa an daskarar da asusun bankinta, kuma ta samu tasgaro a aiki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com