'Na Sha Tsangwama Sosai': Gwamna Ya Tuna yadda Ake Masa Ba'a ba Za a Zaɓi Zabiya ba

'Na Sha Tsangwama Sosai': Gwamna Ya Tuna yadda Ake Masa Ba'a ba Za a Zaɓi Zabiya ba

  • Gwamnan Akwa Ibom, Umo Eno, ya bayyana yadda aka yi masa ba’a yayin da yake kamfe na neman takarar gwamna
  • Mai girma Gwamnan ya ce nuna masa wariya sosai saboda shi zabiya ne a yakin neman zaben 2023 a jihar Akwa Ibom
  • Eno ya ce ya sha wahala tun yana yaro saboda halittasa, amma yau yana karrama masu irin wannan yanayi saboda nuna darajarsu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Uyo, Akwa Ibom - Gwamnan Akwa Ibom, Umo Eno, ya bayyana yadda ya fuskanci izgili da wariya a jiharsa.

Gwamna Eno ya bayyana yadda ya sha wahala sosai kan cewa ba za a zabi zabiya a matsayin gwamna ba.

Gwamna ya bayyana tsangwama da ya sha kafin hawa mulki
Gwamna Umo Eno yayin wani taro da zabiya a birnin Uyo. Hoto: @_PastorUmoEno/ X, Sodiq Adelakun/Getty images.
Source: UGC

A wani taro da aka gudanar a Uyo, gwamnan ya bayyana yadda aka yi amfani da yanayinsa wajen siyasa domin bata masa suna, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

An dauki gwamna 1 a Najeriya, an ba shi lambar yabo ta 'Zabin Jama'a' a kasar Faransa

Yadda ake tsangwanar zabiya a wasu wurare

Zabiya cuta ce ta gado wadda ke haifar da rashin sinadarin 'melanin' a fata, gashi da ido, inda hakan ke haddasa matsalolin gani mai tsanani.

Hakan ya sanya wasu daga cikinsu ke fargabar shiga cikin jama'a saboda yadda wasu ke tsangwamarsu duba da cewa ba su suka halicci kansu a haka ba.

Mutane da dama suna yi wa masu halittar zabiya ba'a wanda ke jawo nuna wariyar launin fata da kuma halitta.

Gwamna ya karrama zabiya a Akwa Ibom

Gwamna Eno wanda aka yi masa ba'a a baya ganin cewa shi zabiya ne ya bayyana irin kimar da masu irin halittar suke da ita.

Ya kuma karrama yara masu irin wannan hali, yana cewa:

“Mutane da ake kira zabiya sun kasance na musamman kuma suna da gwamna na musamman."
“Lokacin da muka fara kamfen, wasu sun ce ba sa son gwamna zabiya sai matata ta ce, kai 'yaro ne na musamman'.”

Kara karanta wannan

Kurunkus: Wike ya fadi matsayarsa kan masu marawa Tinubu baya

Gwamna ya karrama masu halittar zabiya a jiharsa
Gwamna Umo Eno ya bayyana takaici kan yi masa ba'a a baya. Hoto: Pastor Umo Eno.
Source: Facebook

Gwamna ya koka kan nunawa zabiya wariya

Eno ya bayyana cewa ana ware zabiya sau da dama kuma ana musu izgili, har ma ba a ba su dama a bainar jama’a wanda haka tauye hakkinsu.

“Ina tunawa, ba sa ba mu dama a baya, suna kiranmu da sunaye, suna hana mu bayyana a fili. Amma yau Allah ya fito da mu.”

- Cewar Gwamna Eno

Ya ce saboda haka duk inda ya ga mai irin wannan yanayi sai ya mutunta shi, ya kuma nuna cewa su ma suna da daraja, Tribune ta ruwaito.

Gwamnan ya bayyana yadda ya girma a matsayin zabiya, inda ya ce:

“Na fuskanci izgili, cin zarafi da wariya, amma yau ina alfahari.”

Ya ce shi ya sa duk lokacin da ya hadu da mai wannan halitta, sai ya karrama shi domin tabbatar da darajarsa.

Gwamna Eno ya faɗi dalilinsa na komawa APC

Kun ji cewa Gwamna Umo Eno na Akwa Ibom ya fadi dalilansa na komawa jam'iyyar APC inda ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Kwana ya kare: Alkali 'mafi tausayi a duniya' ya rasu yana da shekaru 88

Eno ya ce cire tallafin fetur ya sa gwamnoni suka fi samun kudi, inda ya bayyana alherin da Akwa Ibom ke samu a sakamakon hakan.

Ya ce wannan sauyin siyasa hadaya ce ga Tinubu a ranar Sallah, yana kuma tabbatar da goyon bayansa ga ayyukansa na musamman.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.