Yara Sun Dauko Bam ba Tare da Sani ba a Borno, Mutane Sun Rasa Rayukansu

Yara Sun Dauko Bam ba Tare da Sani ba a Borno, Mutane Sun Rasa Rayukansu

  • Wani bam da aka dauko daga bayan gari bisa rashin sani ya tarwatse a yankin karamar hukumar Konduga ta jihar Borno
  • Rahotanni sun nuna cewa wasu yara ne suka dauko bama-damai ba tare da sani ba, daya daga ciki ya tashi da su yau Litinin
  • Rundunar yan sanda ta samu nasarar kwance wani bam da aka gano a gonar wani manomi, ta ja kunnen mazauna yankin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Borno - Aƙalla mutane biyu ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon fashewar bam da ta auku a ƙaramar hukumar Konduga, Jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa mutum hudu sun samu raunuka sakamakon fashewar bam din a yau Litinin, 18 ga watan Agusta, 2025.

Taswirar jihar Borno.
Hoton taswirar jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Najeriya Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Yadda yara suka dauko bama-bamai a Borno

Leadership ta tattaro cewa wasu yara su shida da ke harkar gwangwan ne suka dauko bama-bamai ba tare da sani ba, a tunaninsu karafa ne da za su sayar su samu kudi.

Kara karanta wannan

Alhaki ya kama su: 'Yan bindiga sun yi hadari bayan karbo makudan kudin fansa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayanai sun nuna cewa yaran su na kan hanyarsu ta zuwa Ajari, wani kauye a cikin ƙaramar hukumar, lokacin da ɗaya daga cikin bama-baman ya fashe.

"Mutane biyu suka rasa rayukansu nan take lokacin da abin ya fashe, yayin da huɗu daga cikinsu ke samun kulawa a Asibitin Gwamnati na Konduga,” in ji wata majiya.

'Yan sanda sun gano bam a gonar manomi

Haka zalika, rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta gano wani bam da aka dasa bai kai ga fashewa ba (UXO) a wata gona a ƙaramar hukumar Dikwa ta jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa an gano shi ne bayan wani manomi mai suna Babagana Kachalla ya kai rahoton wani abu da ya gani a gonarsa.

A cewarsa, bisa umarnin Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Naziru Abdulmajid, an tura tawagar ƙwararrun masu kwance (EOD), inda aka gano cewa bam din Cluster Bomb Unit (CBU) ne mai tsawon mita 2.2 da fadin santimita 30.

Kara karanta wannan

An saki hotunan bam da 'yan sanda suka gano a cikin gonar wani manomi a Borno

Yadda aka kwance bam a gona a jihar Borno

"A bisa ƙa’idar aikin dakarun EOD, an killace wurin yadda ya kamata, daga nan aka binciko inda aka birne mahadar bam din, su ka warware shi cikin nasara," in ji shi.

Kakakin yan sandan ya ƙara da cewa an wayar da kan al’ummar yankin game da hatsarin bama-bamai domin sanin matakan da za su dauka idan suka ci karo da irin waɗannan abubuwa.

Dakarun yan sandan Najeriya.
Hoton jami'an yan sanda a bakin aiki cikin shiri Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Getty Images

Rundunar yan sanda ta sake jaddada aniyarta ta ci gaba da kare lafiyar al’ummar Jihar Borno, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

“Ana shawartar jama’a da su kasance masu kula, kuma su gaggauta kai rahoton duk wani abu ko motsi da suka zaci abin tuhuma ne ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa,” in ji Daso.

Yan sanda sun tare bama-bamai a Kaduna

A wani rahoton, kun ji cewa yan sanda sun yi nasarar dakile yunkurin shiga da bama-bamai da makamai cikin jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

Rigima ta barke a zaben cike gurbin Sanata Ubah da ya rasu, an kama 'yan APC

Rahotanni sun nuna cewa an yi yunkurin safarar makaman zuwa Kaduna ta cikin kayan gwangwan amma dakarun yan sanda suka damke su.

Lamarin ya tayar da hankula, musamman ganin yadda ake shigo da kaya daga yankunan da ke fama da rikicin ‘yan ta’adda.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel