‘Yan Fashi 50 Sun Farmaki Kwalejin Bauchi, Barnar da Suka Yi Ta Sa An Rufe Makarantar

‘Yan Fashi 50 Sun Farmaki Kwalejin Bauchi, Barnar da Suka Yi Ta Sa An Rufe Makarantar

  • Dalibai 10 sun jikkata bayan ‘yan fashi sama da 50 sun kutsa kai hari cikin kwajelin tarayya ta Bauchi a lokacin da daliban ke barci
  • Zanga zanga ta barke a a kofar kwalejin, inda dalibai suka yi kira ga hukumomi da su dauki mataki kan matsalar tsaro a makarantar
  • Bayan faruwar hakan, hukumar makarantar ta rufe kwalejin har sai baba ta gani, inda ta umarci dalibai su kwase dukkan kayansu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Bauchi - Akalla dalibai 10 ne suka samu munanan raunuka yayin da wasu 'yan fashi dauke da makamai suka farmaki dakin kwanan dalibai a Bauchi.

An ce 'yan fashi da yawansu ya haura 50 sun kutsa cikin kwalejin fasaha ta tarayya da ke Bauchi a safiyar ranar Talata, inda suka sassari dalibai.

Kara karanta wannan

Fursunoni sun farmaki jami'an NCoS, sun tsere daga gidan yarin Keffi

'Yan fashi sun farmaki dakin kwanan dalibai a kwalejin tarayya ta Bauchi
Kofar shiga kwalejin tarayya da ke Gwallameji, jihar Bauchi. Hoto: @MySchoolGist
Asali: Twitter

'Yan fashi sun farmaki kwalejin Bauchi

Jaridar The Guardian ta rahoto cewa bayan faruwar lamarin, daliban makarantar sun gudanar da zanga zanga a kofar shiga kwalejin, don nuna bacin ransu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daliban sun jawo tsaikon zirga zirgar ababen hawa a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Tafawa Balewa, yayin da suke kira ga hukumomi su dauki matakin gaggawa.

A cewar daliban, 'yan fashin sun farmaki dakunan kwanan dalibai da misalin karfe 2:00 na safiyar Talata, suna nuna wa dalibai bindiga, tare da sarar wadanda suka yi masu turjiya.

Wasu dalibai da suka yi magana da menam labarai sun ce rashin isasshen tsaro ne ya jawo har 'yan fashin suka samu damar shiga cikin kwalejin.

Ta'asar da 'yan fashin suka yi wa dalibai

Masu zanga zangar, wadanda suka ki barin malamai da sauran ma'aikata shiga cikin makarantar, sun ce babu haske a dakunan kwanan dalibai, wanda ke sa wurin ya yi duhu.

Kara karanta wannan

Sanata ya cire fargaba, ya tona wadanda suke daukar nauyin kisan mutane a Filato

Wani dalibi ya bayyana cewa:

"Muna cikin barci muka fara jin hayaniya daga dakunan da ke kusa da mu. 'Yan fashin da suka haura 50 suka farmake mu da bindigogi da adduna, suna magana da Hausa.
"Duk da cewa ba su kashe ko daya daga cikinmu ba, amma sun ji wa wasu dalibai munanan raunuka. Wani har ya samu matsalar kashin gadon baya."
Hukumar gudanarwar kwalejin fasaha ta tarayya a Bauchi ta rufe makarantar bayan harin 'yan fashi
Dalibai sun gudanar da zanga zanga a kofar kwalejin fasaha ta Bauchi bayan harin 'yan fashi. Hoto: @MySchoolGist
Asali: Twitter

An rufe kwalejin Bauchi bayan harin

Hukumar gudanarwar kwalejin fasaha ta tarayya ta Bauchi ta sanar da rufe makarantar na har sai baba ta gani bayan zanga-zangar daliban da ta barke, inji rahoton The Nation.

A cikin wata sanarwa a ranar Talata, magatakardar kwalejin, Alhaji Kasimu Salihu ya ce makarantar ta samu rahotannin harin da 'yan fashi suka kai wa daliban.

"Mun fahimci cewa wasu bata gari da ke nufin dalibai da makarantar da sharri sun mamaye wannan zanga zanga tare da kokarin rikidar da ita zuwa wata fitina."

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Ƴan bindiga sun kai hari 'Gidansu Atiku,' sun yi garkuwa da mata

- Alhaji Kasimu Salihu.

Hukumar gudanarwar ta bukaci dukkanin dalibai su fice daga dakunan kwanansu cikin awanni biyu, tana mai cewa dole ta rufe makarantar zuwa wani lokaci gaba saboda matsalar tsaro.

'Yan bindiga sun sace daliban kwaleji

A wani labarin, mun ruwaito cewa, 'yan bindiga sun yi aika-aika a Delta yayin da suka sace wasu dalibai mata masu yin karatu a wata kwalejin ilmi.

Miyagun sun sace daliban ne a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa birnin Asaba, babban birnin jihar Delta domin yin wasu abubuwa.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa an sako daya daga cikin matan da aka sace bayan da aka biya miliyoyim kudi a matsayin kudin fansa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com