Kebbi: Gwamna Ya Ƙirƙiro Sabuwar Masarauta, Ya Naɗa Sababbin Hakimai 2

Kebbi: Gwamna Ya Ƙirƙiro Sabuwar Masarauta, Ya Naɗa Sababbin Hakimai 2

  • Gwamnan jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Ƙauran Gwandu) ya raba masarautar Maiyama zuwa gida biyu tare da naɗa sababbin hakimai biyu
  • Kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu na jihar, Alhaji Garba Dutsinmari ya ce an cire masarautar hakimin Sarandosa daga Maiyama
  • A wata sanarwa da kwamishinan ya fitar, ya ce Gwamna ya amince da naɗin Dr. Faruk Maiyama a matsayin Sarkin Gabas Sarandosa kuma hakimi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kebbi - Gwamnatin Jihar Kebbi ƙarƙashin jagorancin Gwamna Nasir Idris ta amince da ƙirƙirar sabuwar masarautar Sarandosa a ƙaramar hukumar Maiyama

Gwamnatin Kebbi ta ce wannan dai wani ɓangare ne na sabon tsarin da ta ɗauko da nufin daidaita harkokin mulki da sarauta a jihar Kebbi da ke Arewa maso Yamma.

Gwamna Nasir Idris Kauran Gwandu.
Gwamnan Kebbi ya kirƙiro sabuwar masarauta, ya nada hakimai 2 Hoto: Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu
Source: Facebook

Jaridar Punch ta rahoto cewa hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi da Masarautu, Alhaji Garba Dutsinmari, ya sanya wa hannu.

Kara karanta wannan

Abubuwa 9 da kwamitin bincike ya gano game da kwamishinan da da ake zargi a Kano

Kwamishinan ya rabawa manema labarai wannan sanarwa a Birnin Kebbi ranar Laraba, 6 ga watan Agusta, 2025.

Gwamnan Kebbi ya ƙirƙiro sabuwar masarauta

A cewar sanarwar, Gwamna Nasir Idris ya amince da ciro masarautar Sarandosa daga ƙaramar hukumar Maiyama, wadda ke ƙarƙashin Sarkin Kudun Maiyama

Kwamishinan ya ƙara da cewa garin Sarandosa ne zai kasance fadar sabuwar masarautar da aka ƙirƙira a yankin Maiyama.

Yankin masarautar Sarandosa zai ƙunshi garuruwa guda biyar kamar haka: Gubba, Sarandosa, Acikaratu Ubandawaki, Acikaratun Dodo da kuma Tsalibi.

Dalilin raba yankin hakimin Maiyama gida 2

Garba Dutsinmari ya bayyana cewa ƙirƙirar masarautar ya zama dole ne sakamakon ci gaban yankin da kuma buƙatar inganta gudanarwar mulki da sarauta.

Ya ce duba da yadda yankin ke ci gaba, akwao buƙatar kawo sauyi ta hanyar raba alhakin shugabanci domin samun sauƙi na gudanarwa.

Gwamna Idris ya naɗa sababbin hakimai 2

Gwamnatin jihar Kebbi ta nada Dr. Faruk Maiyama a matsayin hakimin farko na sabuwar masarautar Sarandosa, tare da ba shi sarautar gargajiya ta Sarkin Gabas na Sarandosa.

Kara karanta wannan

Belin dilan ƙwaya: Kwamishinan Abba a jihar Kano ya yi murabus

Haka kuma, an sake naɗa Haliru Maiyama a matsayin sabon Hakimin Maiyama da aka sake fasalinta wa a yanzu, inda zai ci gaba da riƙe sarautar Sarkin Kudun Maiyama.

Gwamna Nasir Idris Kauran Gwandu.
Gwamnatin Kebbi ta kara masarautar Hakimi a yankin karamar hukumar Maiyama Hoto: Nasir Idris Kauran Gwandu
Source: Facebook

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa yankin masarautar Maiyama a yanzu za ta ƙunshi ƙauyuka guda bakwai, wato Dangaladıman Maiyama, Yarıman Maiyama, Giwatazo, Kurya, Rafintofa, Zara Birni, da kuma Idiga.

An naɗa sababbin hakimai 5 a jihar Katsina

A wani rahoton, kun ji cewa Sarkin Katsina, Mai Martaba Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya naɗa sababbin hakimai shida da aka ƙirƙira a jihar.

Sakataren masarautar Katsina, Alhaji Belli Ifo ne ya bayyana waɗanda aƙa naɗa a matsayin hakimai a wata sanarwa da ya fitar ramar Asabar da ta shuɗe, 2 ga watan Agusta, 2025.

Ɗan mai girma gwamnan Katsina, Muhammad Dikko Umaru Raɗɗa da tsohon minista, Hadi Sirika na cikin waɗanda aka naɗa a matsayin sababbin hakimai a jihar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262