Abin Mamaki: Farida Sultana da Wasu Mata 'Yan Arewa 2 Sun Shiga Shirin BBNaija

Abin Mamaki: Farida Sultana da Wasu Mata 'Yan Arewa 2 Sun Shiga Shirin BBNaija

Abuja – Gasar Big Brother Naija (BBNaija) ta shiga zangonta na 10 a 2025 cikin sabon salo mai zafi, inda aka fara da mata 15 kacal a daren ƙaddamarwa na Asabar.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Daga cikin mata 15 da za su fafata a wannan gasar ta bana, akwai guda uku da suka fito daga jihohin Arewa; Kaduna, Benue sda kuma Adama - abin da ba a saba gani ba.

Wasu mata uku daga jihohin Arewa sun shiga shirin BBNaija zango na 10
Sultana Ibrahim, Sonia Amako, Josephine Iwoh daga jihohin Adamawa, Benue da Kaduna sun shiga shirin BBNaija zango na 10. Hoto: @TWEETORACLE
Source: Twitter

An fara shirin BBNaija zango na 10

Channels TV ta rahoto cewa matan 15 da suka fito daga kabilu da jihohi daban-daban sun shiga gidan 'Biggie' domin kafa tarihi tare da kawo sabon salo da nishadi cikin shirin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An buɗe zangon bana da raye-rayen mawaki Fido (da waƙar “Joy Is Coming”), alamar cewar wannan kakar za ta kasance cike da dariya, rudani da kuma sabon nishadi.

Kara karanta wannan

Za a caɓa: Gwamnatin Tinubu ta fara ɗiban matasa aiki domin rage zaman banza

Ebuka Obi-Uchendu, wanda aka fi sani da 'gwanin ado', ya shiga gidan da kaya biyu masu jan hankali: Daya irin na Osuofia da wasu manyan kaya da ke tuna wa da Sarki Sunny Ade.

BBNaija S-10: Mata 15 sun shiga gidan Biggie

A yayin da aka shirya shigar maza ranar Lahadi, 27 ga Yuli, hankula sun karkata kan matan da za su fafata a shirin, wadanda suka shiga gidan Biggie a ranar Asabar.

Daga Zita zuwa Isabella, daga Joanna zuwa Big Soso, kowacce ta shiga gidan da kuzari, kyau da salo, alamar tana shirye don yin abin da zai sa ta lashe gasar.

Wannan zangon na musamman ne, domin shi ne zangon bikin cika shekara 10 da kafuwar gasar BBNaija, wanda aka sanya masa kyautar N150m ga zakaran shirin.

Sabon gida, sababbin dokoki, da sabuwar rayuwa; abin da ke jiran wadannan zafafan mata. Lokaci kuma ya yi da masu kallo za su ba idanuwansu abinci.

Mata 3 'yan Arewa da suka shiga shirin BBNaija

A gasar BBNaija ta bana, akwai mata uku da suka shiga, wadanda sun fito ne daga jihohin Arewacin kasar; Kaduna, Benue da kuma Adamawa - abin da ba a saba gani ba.

Kara karanta wannan

2027: APC ta tsorata da ake shirin kawo sauyi kan zaɓen shugaban ƙasa, gwamnoni

Legit Hausa ta yi bayani game da 'yan wasan:

Sonia Amako (Big Soso) ta shiga shirin BBNaija zango na 10 daga jihar Kaduna
Sonia Amako (Big Soso) ta ce ta shiga shirin BBNaija domin tallata Arewacin Najeriya ga duniya. Hoto: @TWEETORACLE
Source: Twitter

1. Big Soso (Sonia Amako), 28 – Kaduna

Sonia Amako, wadda za a rika kiranta da Big Soso a shirin, ta kasance kwararriyar mai dafa abinci kuma lauya da ta yi karatu a Burtaniya.

Gidan talabijin na DSTV ya rahoto Big Soso ta bayyana cewa ta shiga shirin BBNaija ne domin:

"Ina son na zama gadar da ta hade Arewa da sauran sassan Najeriya ta hanyar nuna karfin hali, jajurcewa da kyawun da akasan yankinmu yana da shi.
"Ina so 'yan mata da ke tasowa su dauki darasi a kaina, cewa za su iya yin aiki tukuru domin cika mafarkansu, su gina kasuwanci, su taimakawa al'umma, kuma su kare al'adunsu."
Joanna (Josephine Iwoh) ta shiga shirin BBNaija zango na 10 daga jihar Benue
Joanna (Josephine Iwoh) ta ce ta shiga shirin BBNaija ne domin nunawa duniya irin baiwarta. Hoto: @TWEETORACLE
Source: Twitter

2. Joanna (Josephine Iwoh), 21 – Benue

Josephine Iwoh, wacce za a rika kira da Joanna a gasar, ta kasance sarauniya a gasar kyawawa da ta koma harkar kasuwanci. Joanna ba ta jin tsoron bayyana ra’ayina.

Kara karanta wannan

An cakawa jami'ar NSCDC wuƙa a Abuja, asibitoci sun ƙi karɓarta har ta mutu

Joanna ta bayyana cewa ta shiga shirin BBNaija zango na 10 domin:

"Na saba taka rawa a shirye-shiryen jama'a, amma shiga ta wannan shirin zai ba ni damar nunawa duniya irin baiwar da Allah ya ba ni.
"A cikin wannan gidan, mutane za su san wacece Josephine, za su gane rawar kan Josephine, za su fahimci karfin zuciya da jarumtar Josephine, kuma za su san kyawawan dabi'u na da ma akasin hakan.
"Na shiga shirin don na gwada kaina, na koya daga mutanen da suka fito daga wurare daban daban, in kuma koyi juriya daga gwaje-gwajen da zan gamu da su a gidan."
Sultana (Farida Sultana Ibrahim) ta shiga shirin BBNaija zango na 10 daga jihar Adamawa
Farida Sultana Ibrahim ta ce ta shiga shirin BBNaija domin ta gwada karfin kwakwalwa da juriyarta ga sabon kalubale. Hoto: @TWEETORACLE
Source: Twitter

3. Sultana (Farida Sultana Ibrahim), 25 – Adamawa

Farida Sultana Auduson Ibrahim, wacce za a rika kira da Sultana a shirin, ta kasance kyakkyawa, mai cike da kuzari, baiwa da kuma hangen nesa.

BBNaija Daily ya rahoto Farida Sultana Auduson Ibrahim ta bayyana cewa ta shiga shirin BBNaija na bana ne domin:

"Ni mai son shiga bakon abu ne, kullum ina so na gwada karfin kwakwalwa da tunani na, in kuma gwada mizanin sauyin da ruhi da jikina za su iya dauka.

Kara karanta wannan

'Yan Zamfara sun huro wuta, suna so Dauda Lawal ya sauka daga kujerar gwamna

A shirye nake na tunkari sabon kalubale, kuma ina da yakin cewa kalubalen zai koya mani darasin da zan gina rayuwata da shi.
"Ina kuma son na hadu da mutanen da suka fito daga bigiren rayuwa daban-daban, mu san labarin juna, mu koyi dabi'un juna, mu kuma nunawa duniya karfi da izzar Arewacin Najeriya."

Sauran mata a wasan BBNaija

Bayan bayani game da 'yan mata uku da suka fito daga Arewa, akwai kuma jerin sauran matan da suka shiga shirin BBNaija zango na 10:

4. Zita (Elizabeth Oloruntola), 24 – Lagos

5. Gigi Jasmine (Nicole Simon–Ogan), 31 – Akwa Ibom

6. Ivatar (Ifeyinwa Okafor), 37 – Anambra

7. Sabrina Idukpaye, 32 – Edo

8. Mide (Ayomide Iwasokun), 23 – Ondo

9. Dede (Precious Ashiogwu), 23 – Delta

10. Doris Okorie, 33 – Imo

11. Isabella (Esther Georgewill), 29 – Rivers

12. Imisi (Opeyemi Ayanwale), 23 – Oyo

13. Ibifubara Davies, 28 – Lagos

14. Tracy (Uchenna Ekwe), 27 – Anambra

15. Thelma Lawson, 26 – Rivers

'Shirin BBNaija wakilin shaidan ne' - MURIC

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda sun kai farmaki a Neja, an yi awon gaba da bayin Allah

A wani labarin, mun ruwaito cewa, kungiyar hare hakkin musulmai ta MURIC ta bayyana goyon bayanta ga kawo karshen shirin BBNaija.

A lokuta da dama kungiyar ta sha bayyana rashin amincewarta da shirin mai nuna abubuwan da basu dace da tarbiyya ba, har ma ta kira BBNaija da 'wakilin shaidan.'

MURIC ta koka da yadda wani gwamna ya kwashi kudaden jama'a da gida ya ba wanda ya lashe wasan BBNaija, ba tare da la'akari da tasirin hakan ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com