Dangote Ya Yi Murabus daga Shugabancin Kamfaninsa, Ya Faɗi Inda Zai Maida Hankali

Dangote Ya Yi Murabus daga Shugabancin Kamfaninsa, Ya Faɗi Inda Zai Maida Hankali

  • Alhaji Aliko Dangote ya yi murabus daga shugabancin kamfaninsa na siminti domin mayar da hankali wani bangare
  • Dangote ya ajiye aikin ne a ɓangaren sminiti don mayar da hankali kan matatar mai, sinadarai da hulda da gwamnati
  • Emmanuel Ikazoboh zai maye gurbin Dangote a matsayin sabon shugaban kamfanin, yayin da Hajiya Mariya Dangote ta shiga kwamitin kamfanin

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Kamfanin Dangote ya tabbatar da murabus din shugabansa na sashen siminti, Alhaji Aliko Dangote.

Kamfanin simintin ya ce Aliko Dangote, wanda shi ne mai hannun jari mafi girma kuma wanda ya kafa kamfanin, ya ajiye aiki.

Dangote ya yi murabus daga shugaban kamfaninsa
Dangote ya ajiye mukamin shugaban kamfaninsa na siminti. Hoto: Dangote Group.
Source: Getty Images

Dangote ya yi murabus daga kamfanin siminti

Hakan na cikin wata sanarwa da shugaban sashen hulda da jama’a na Dangote Anthony Chiejina ya fitar, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

Babbar magana: An yi barazanar kama gwamnan babban bankin Najeriya, CBN

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Chiejina ya ce Dangote ya bar mukamin ne don maida hankali kan bangaren kamfanin matatar mai.

Ya ce zai fi mayar da hankali ne kan matatar mai ta Dangote, kamfanin sinadarai da na takin zamani, da kuma hulda da gwamnati.

An naɗa wanda zai maye gurbin Dangote?

Chiejina ya bayyana cewa Emmanuel Ikazoboh, wanda ya kasance mamba mai zaman kansa a kwamitin kamfanin, shi ne aka nada sabon shugaban kamfanin.

Hakazalika, mai magana da yawun kamfanin ya ce an nada Hajiya Mariya Aliko Dangote a kwamitin, yayin da Dorothy Ufot ta yi ritaya.

Ya ce:

“Shahararren ɗan kasuwa kuma wanda ya kafa 'Dangote Cement Plc', Aliko Dangote, ya sanar da murabus dinsa daga shugabancin kamfanin.
“Ya bar mukaminsa ne don maida hankali kan matatar mai, sinadarai, takin zamani da hulda da gwamnati don cimma burin kasuwanci na shekaru 5.
“Kwamitin simintin Dangote ya sanar da nadin Emmanuel Ikazoboh a matsayin sabon shugaban kamfanin. Haka kuma an nada Hajiya Mariya a kwamitin.

Kara karanta wannan

Matasa 50,000 za su samu aiki a hadakar noman da Dangote ya yi da Neja

Dangote ya bar mukaminsa Na shugabancin kamfanin siminti
Bayan shafe shekaru, Dangote ya yi murabus a kamfanin siminti. Hoto: Getty Images.
Source: UGC

Gudunmawar da Aliko Dangote ya ba kamfanin

Chiejina ya ce Aliko Dangote ya ba da gudunmawa a masana'antar, inda hangen nesansa ya sauya harkar siminti a Najeriya da Nahiyar Afirka baki ɗaya, Punch ta ruwaito.

“Dangote ya fara ne da burin samar da isasshen siminti a Najeriya da Afirka. Ya cika burin, har ma ya wuce shi.
“Kamfanin simintin Dangote na da ƙarfin sarrafa tan miliyan 52 a Afirka gaba ɗaya, inda Najeriya ke da tan miliyan 35.25.
“An fara gina sababbin masana’antu a Cote d’Ivoire da Itori, Nigeria. Idan sun kammala, ƙarfin zai kai tan miliyan 61.
“A ƙarƙashin jagorancinsa, kamfanin ya samu mafi yawan kuɗin shiga da ribar EBITDA a tarihinsa."

- Inji Chiejina

Dangote ya yi murabus daga kamfanin sukari

Kun ji cewa Alhaji Aliko Dangote ya ajiye aiki a matsayin shugaban hukumar kamfanin sukari na Dangote bayan shafe shekaru 20 yana jagoranci.

Kara karanta wannan

Cacar baki ta kaure tsakanin Akpabio da Barau da aka zo tantance wani tsohon sanata

Kamfanin ya ce Dangote ya jagoranci manyan ayyuka a jihohin Adamawa, Taraba da Nasarawa don karfafa samar da sukari a gida da rage shigo da kaya.

Tsohon shugaban bankin Ecobank, Arnold Ekpe ya gaji kujerar Dangote a matsayin sabon shugaban, bayan cikakken tsarin tantancewa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.