Garambawul: Gwamna Ya Rantsar da Sababbin Kwamishinoni 6, Ya Sauya Muƙaman Wasu
- Gwamna Peter Mbah ya rantsar da sababbin kwamishinoni shida tare da sauya wasu ma'aikatu don ƙarfafa aiki a jihar Enugu
- Majalisar jihar Enugu ce ta fara tantance sababbin kwamishinonin da suka haɗa da na ayyuka, lafiya, makamashi da kasuwanci
- Gwamna Mbah ya bukaci sababbin kwamishinonin da su fara aiki nan take, yana mai cewa gwamnati na da manyan burace-burace a gabanta
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Enugu – A ranar Laraba, Gwamna Peter Mbah na jihar Enugu ya sauya mukaman wasu kwamishinoni uku tare da rantsar da sababbin kwamishinoni shida da aka naɗa.
Gwamna Mbah ya kuma raba muƙamai ga sababbin kwamishinonin bayan da Chizoba Ogbodo, wakiliyar ma'aikatar shari'a, ta rantsar da su a gidan gwamnati da ke Enugu.

Source: Twitter
Hakazalika, Gwamna Mbah ya rantsar da Godwin Anigbo a matsayin shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Enugu, inji rahoton Premium Times.

Kara karanta wannan
Cacar baki ta kaure tsakanin Akpabio da Barau da aka zo tantance wani tsohon sanata
An gudanar da bikin rantsar da kwamishinonin ne bayan majalisar jihar Enugu ta tantance kuma ta tabbatar da sunayen wadanda aka naɗa.
An rantsar da sababbin kwamishinoni 6
A makon jiya ne aka rahoto cewa Gwamna Mbah ya mika sunayen kwamishinonin da yake so ya nada zuwa gaban majalisar domin tantancewa.
Sabbin kwamishinonin da aka rantsar da ma'aikatar su:
- Benjamin Okoh - Ayyuka da abubuwan more rayuwa
- Benedett Okoli - Bunkasa jama'a da kawar da talauci
- Franklin Ogbonna - Harkokin makamashi da ma’adanai
- Samuel Ogbu-Nwobodo - Kasuwanci, zuba jari da masana’antu
- Ben Collins Ndu Jr. - Harkokin Ruwa
- George Ugwu - Lafiya
Garambawul a ma'aikatun jiha Enugu
George Ugwu ya maye gurbin Emmanuel Obi da ya riƙe kujerar kwamishinan lafiya tun daga shekarar 2015 a zamanin tsohon gwamna Ifeanyi Ugwuanyi.
An sauya ma Felix Nnamani mukami daga kwamishinan ma’aikatar ruwa zuwa ma’aikatar kwadago da ayyuka, inda zai maye gurbin Chika Ugwuoke wanda aka tsige daga kujerar makon da ya gabata.
Haka nan, an dage Gerald Otiji daga ma’aikatar ayyuka zuwa ma’aikatar gidaje, yayin da Malachy Agbo ya koma ma’aikatar yada labarai daga ma’aikatar bunkasa jama'a da yaki da Talauci.
Malachy Agbo ya maye gurbin Aka Eze, wanda ya yi murabus domin tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukumar Udenu, kuma ya yi nasara.

Source: Twitter
“A fara aiki cikin gaggawa” – Gwamna Mbah
A yayin rantsar da kwamishinonin, Gwamna Mbah ya jaddada cewa babu lokacin ɓatawa, kuma ya bukace su da su fara aiki nan take.
Ya ce cikin shekaru biyu da suka gabata, gwamnatinsa ta lasawa jama’ar jihar da ma Najeriya gaba ɗaya zuma a baki kan manyan ayyukanta, don haka ba za ta gaza a kowanne fanni ba.
A cewarsa:
“Ya zama wajibi a gare ku ku fara aiki ba tare da ɓata lokaci ba, babu lokacin shakatawa ko hutu.
“Mun tsara manyan buruka masu yawa, kuma kowace ma’aikata za ta taka muhimmiyar rawa wajen cimma waɗannan buruka.”
Uba Sani ya rantsar da sababbin kwamishinoni
A wani labarin, mun ruwaito cewa, Gwamna Uba Sani ya yi nadin sababbin kwamishinoni domin inganta shugabanci a jihar Kaduna.
Mai girma Gwamna Uba Sani ya nada Farfesa Abubakar Sambo a matsayin kwamishinan Ilimi, sannan aka sauyawa Farfesa Sani Bello ma’aikata.
Gwamnan ya ce yana sa ran sababbin kwamishinonin za su kawo sauyi a ma’aikatunsu tare da samar da hanyoyin magance matsalolin jihar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

