Manoma na cikin Tashin Hankali, Ambaliyar Ruwa Ta Yi Barna a Garuruwa 7 na Kebbi

Manoma na cikin Tashin Hankali, Ambaliyar Ruwa Ta Yi Barna a Garuruwa 7 na Kebbi

  • Ambaliyar ruwa a Kebbi ta lalata gonakin shinkafa a Yauri, Shanga da Ngaski, inda hakan ya jefa dubban manoma cikin damuwa
  • Ahmed Sarkin Yaki ya tabbatar da aukuwar ambaliya a garuruwan Kwanji, Gebbe, Nasara, Ishe, Tungan Hakimi Mamuda, Buro da Kurdoso
  • Kebbi da wasu jihohin da ke makwabtaka da ita kamar Neja, Sokoto da Kwara sun fuskanci ambaliyar ruwa mai muni a 2024 da 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kebbi - Ambaliyar da ta auku a Kebbi sakamakon cika da tumbatsar koguna ta lalata gonakin shinkafa a ƙananan hukumomin Yauri, Shanga da Ngaski na jihar.

An ce ambaliyar ta lalata gonakin shinkafa da dama a ƙananan hukumomin uku da ke ƙarƙashin masarautar Yauri, wanda ya jefa manoma cikin tashin hankali.

Ambaliyar ruwa a Kebbi ta lalata gonakin shinkafa a garuruwa 7
Barnar da ambaliyar ruwa ta yi a Borno a shekarar 2024. Hoto: Audu Marte
Source: Getty Images

Ambaliya ta yi barna a jihar Kebbi

Kara karanta wannan

'Ku shirya': Kano, Bayelsa da jihohi 33 da za a sheka ruwa da iska mai karfi

Wani ɗan asalin yankin, Ahmed Sarkin Yaki ne ya tabbatar da aukuwar wannan iftila’in a Birnin Kebbi, yayin da yake zantawa da jaridar Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa, garuruwan da ambaliyar ta yi wa manoma barna sun haɗa da Kwanji, Gebbe, Nasara, Ishe, Tungan Hakimi Mamuda, Buro da Kurdoso.

“Muna zargin ruwan kogunan Dolekaina, Jega da Tondi Gada ne ya balle, ya jawo ambaliiya a garuruwan.
“Muna roƙon shugabannin ƙananan hukumomin Yauri, Shanga da Ngaski da su kawo ɗauki ga manoman da ambaliya ta shafa."

- Ahmed Sarkin Yaki.

Kalubalen ambaliya a jihar Kebbi

Jihar Kebbi na fuskantar mummunar ambaliya a ‘yan shekarun nan, lamarin da ke da tasiri sosai ga fannin noma, musamman shinkafa, wadda jihar ke kan gaba wajen nomawa a ƙasar.

A shekarar 2024, ambaliya ta shafi ƙananan hukumomi 16 daga cikin 21 na jihar Kebbi, ciki har da Yauri, Shanga da Ngaski, inda ta lalata hekta 858,000 na gonaki, da amfanin gona kamar su shinkafa, masara da dawa.

Iftila’in ya yi sanadin mutuwar mutane 29, tare da raba dubban mutane da muhallansu, lamarin da ya haifar da fargabar ƙarancin abinci, inji rahoton Channels TV.

Kara karanta wannan

Tanka makare da fetur ta yi hatsari, ta kama da wuta kusa da gidan man NNPCL

Ambaliya a jihohin da ke makwabtaka da Kebbi

Jihar Neja:

A watan Afrilu 2025, an samu ambaliya sakamakon ballewar ruwa daga dam ɗin Jebba, wanda ya shafi manoman rani fiye da 5,000, tare da lalata hekta 10,000 na gonakin shinkafa a karamar hukumar Mokwa kaɗai.

Jihohin Arewa musamman wadanda ke kusa da gabar tekuna na fuskantar ambaliya a kai a kai
Wasu yankunan Maiduguri da suka nutse a cikin ruwa sakamakon ambaliya a 2024. Hoto: Audu Marte
Source: Getty Images

Hakan ya shafi manoma a jihohin Kebbi, Sokoto, Katsina da Kano, inda aka yi asarar biliyoyin Naira tare da raba mutane fiye da 6,400 da muhallansu.

A wata ambaliyar da ta sake faruwa a Mokwa a watan Mayun 2025, an ce sama da mutane 150 suka mutu, yayin wa sama da mutane 3,500 suka rasa muhallansu, inji rahoton Aljazeera.

Jihohin Sokoto da Kwara:

Ambaliya ta 2024 da ke da nasaba da ruwa daga dam ɗin Goronyo da Kogin Rima ta haddasa asarar amfanin gona a Sokoto.

Ambaliyar ruwa a watan Afrilu 2025 daga dam ɗin Jebba ta shafi jihar Kwara sosai, inda aka yi asarar gonakin shinkafa da dama.

Kara karanta wannan

Kogi: Malamin jami'a ya mutu yana tsakiyar lalata da ɗalibarsa, an ga gawarsa a otal

Ambaliya ta yi barna a jihohi 2

A wani labarin, mun ruwaito cewa, ambaliyar ruwa ta lalata gonakin al’umma a sassa daban-daban na jihohin Kebbi da Neja da ke Arewacin kasar nan.

Hukumar N-HYPPADEC ta bayyana tausayinta ga waɗanda iftila’in ya shafa tare da jinjina wa gwamnatin tarayya bisa ware Naira biliyan 3 domin rage radadin lamarin.

Kusan kowace shekara Najeriya na fuskantar ambaliya a jihohi da dama, musamman waɗanda koguna da ruwa ke gudana a cikinsu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com