Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda Ya Yi Hatsari, An Ji Halin da Yake Ciki

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda Ya Yi Hatsari, An Ji Halin da Yake Ciki

  • Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Raɗɗa ya gamu da hatsarin mota a kan titin Daura zuwa Katsina da yammacin yau Lahadi
  • Mai magana da yawun gwamnan, Ibrahim Kaula Mohammed ya ce hatsarin ƙarami ne kuma Gwamna Raɗɗa na cikin ƙoshin lafiya
  • Duk da dai ba a bayyana abin da ya haddasa hatsarin ba, Ibrahim Kaula ya ce Malam Dikko bai ji wani mummunan rauni a hatsarin ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Rahotannin da muke samu daga jihar Katsina na nuna cewa gwamnan jihar, Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya yi hatsarin mota a hanyar Daura zuwa Katsina.

Gwamnatin Katsina ta tabbatar da aukuwar lamarin, tana mai cewa hatsarin ƙarami ne kuma mai girma gwamna yana cikin ƙoshin lafiya.

Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radɗa.
Hatsarin mota ya rutsa da gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Radda Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Mai magana da yawun gwamnan Katsina, Ibrahim Kaula Muhammed ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook a daren Lahadi.

Kara karanta wannan

An samu karaya yayin da gwamna Radda da jami'ansa suka yi hadari

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wane hali gwamnan jihar Katsina ke ciki?

Ibrahim ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya tsira, bai samu wani rauni mai tsanani a hatsarin ba, kuma yana cikin ƙoshin lafiya.

"Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya gamu da wani ƙaramin hatsarin mota da yammacin yau a kan hanyar Daura zuwa Katsina, yayin da yake gudanar da ayyukan gwamnati domin hidimar al’umma.
"Muna farin cikin tabbatar wa da jama’a cewa Gwamna Radda na cikin koshin lafiya kuma yana cikin yanayi mai kyau, ba tare da samun wani rauni mai tsanani ba.
"Gwamna Radda na cikin kwarin gwiwa, kuma ya bayyana godiyarsa ga Allah Maɗaukakin Sarki bisa kariyar da ya ba shi, da kuma godiya ga al’ummar Katsina da duk masu fatan alheri bisa addu’o’insu da nuna damuwarsu.

- Ibrahim Kaula Mohammed.

Gwamnan Katsina, Malam Dikko Radda.
Gwamnatin Katsina ta ce Malam Dikko Radda na cikin koshin lafiya bayan hatsarin mota Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Me ya haddasa hatsarin Gwamna Raɗɗa?

Majiyoyi daga yankin sun nuna cewa Gwamna Dikko na tare da shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin Katsina a cikin motar lokacin da hatsarin ya faru.

Kara karanta wannan

Gwamnan Katsina Dikko Radda ya yi bayani daga asibiti bayan haɗarin mota

Gwamnatin Katsina ba ta bayyana ainihin abin da ya haddasa hatsarin ba zuwa yanzu, sai dai ance tuni aka garzaya da Malam Dikko Raɗda zuwa Asibiti a Daura.

Tuni dai al'ummar jihar Katsina suka fara yiwa gwamnan addu'o'in kariya da kuma tsarin Allah SWT daga faruwar irin wannan al'amari a nan gaba.

Jaridar Mobile Media Crew ta bayyana cewa an sallami Gwamna Dikko Raɗɗa daga asibiti a Daura sakamakon babu wani rauni mai tsanani a tattare da shi.

An ba Gwamna Radda lambar yabo

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya lashe lambar yabo ta gwamnan da ya fi kowane aiki a shekarar 2025.

An karrama Gwamna Radda ne bisa namijin ƙoƙarin da yake yi wajen sauya Jihar Katsina ta fuskar inganta ababen more rayuwa, ilimi, lafiya, tsaro da ƙarfafa tattalin arziki.

Gwamnan ya ce ya sadaukar da wannan kyauta ga jajirtattun mata, matasa masu buri, ma’aikata masu himma da kuma daukacin al’ummar Jihar Katsina.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262