An Shiga Firgici a Katsina: Ƴan Bindiga Sun Sace Wani Kansila kuma Ƙanin Ciyaman

An Shiga Firgici a Katsina: Ƴan Bindiga Sun Sace Wani Kansila kuma Ƙanin Ciyaman

  • Wani kansila a Katsina, Buhari Aliyu, da abokinsa Nura Kaura sun fada hannun ’yan bindiga a kan hanyarsu ta komawa Daudawa
  • Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa ’yan bindigar sun sace su ne a hanyar Funtua zuwa Sheme, ba a cikin garin Daudawa ba
  • Ana kuma zargin cewa wani ke bibiyar motar kansilan yana baiwa ’yan bindiga bayani, yayin da har yanzu ba a tuntubi iyalansa ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Katsina - 'Yan bindiga sun yi garkuwa da kansilar gundumar Daudawa da ke karamar hukumar Faskari, jihar Katsina a ranar Litinin 14 ga watan Yulin 2025.

An sace kansilan mai suna Buhari Aliyu Daudawa tare da abokinsa Nura Kaura Wanzan da wasu mutane a hanyarsu ta komawa Daudawa daga Funtua.

Kara karanta wannan

London Clinic: Abubuwan mamaki game da asibitin da Muhammadu Buhari ya rasu

'Yan bindiga sun yi garkuwa da kansilan Daudawa, Buhari Aliyu a ranar Litinin
Surajo Aliyu, kansilan Daudawa da 'yan bindiga suka yi garkuwa da shi. Hoto: Buhari Aliyu Daudawa
Source: Facebook

An yi garkuwa da kansila a Katsina

Wani mazaunin garin Daudawa, Mallam Muhammad Salihu ya shaidawa Legit Hausa cewa 'yan bindigar sun yiwa kansilar kwanton bauna a yankin Dankama da ke hanyar Funtua zuwa Sheme.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mallam Muhammad ya karyata rahotannin da wasu kafafen watsa labarai ke yadawa cewa har cikin garin Daudawa 'yan bindigar suka shiga suka tafi da Hon. Buhari Aliyu.

"Ba cikin Daudawa suka dauke shi ba. Nan wajen burtsatse suka dauke shi, kwarin nan na wajen garin Dakamawa suka tare su, suka tafi da su,"

- A cewar Mallam Muhammad.

Mazaunin garin Daudawan ya ce suna zargin wani 'infoma' (mai ba 'yan bindiga bayanai) ne ya rika bibiyar motar kansilan, yana ba miyagun bayanai har suka kama shi.

Kanin ciyaman din Faskari aka sace

Mallam Muhammad ya kara da cewa:

"Wallahi wani ne ke binsa, don har waya ma ya kira, ya ce akwai wanda yake bibiyarsu. Amma ya ce a kyale shi har sai sun ga yadda ta kwaranye, in ya so sai a gano wanene shi."

Kara karanta wannan

Ana ci gaba da bayyana ayyukan alheran Buhari, Malami faɗI abin da ya sani

Ya ce akwai wasu 'yan Daudawa da aka yi garkuwa da su a kwanan baya, amma an sako su jiya Laraba bayan biyan sama da N6m da sabon babur.

Hon. Buhari Aliyu ya lashe zaben kansila a gundumar Daudawa karkashin APC a zaben ciyamomi da kansiloli da aka gudanar a jihar Katsina a watan Fabrairun 2025.

Yayansa, wanda suke uba daya, Surajo Aliyu Daudawa shi ne ya lashe shugaban karamar hukumar Faskari a zaben da aka gudanar.

"Yan sanda ba su bayar da wani rahoto game da sace kansilan da aka yi ba
IGP Kayode Egbetokun, babban sufetan 'yan sandan Najeriya. Hoto: @PoliceNG
Source: Facebook

Ba a ji daga bakin rundunar 'yan sanda ba

An fahimci cewa har yanzu 'yan bindigar ba su tuntubi iyalan dan siyasar ba, kuma ba a san inda suka kai shi ba tsawon wadannan kwanaki.

Legit Hausa ba ta samu jin ta bakin kakakin rundunar 'yan sandan Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu game da wannan lamarin ba har zuwa lokacin wallafa rahoton.

Da wakilin jaridar ya kira kakakin 'yan sandan a waya, sai ya aiko masa da sakon cewa 'ba zai iya yin magana a yanzu ba,' kuma bai maido da amsar sakon da aka aika masa ba.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Yadda aka fito da gawar Buhari daga jirgi da manyan mutanen da aka gani

Mutanen Faskari sun kama 'yan bindiga

A wani labarin, mun ruwaito cewa, 'yan bindigar da suka kai hari yankin Tafoki da ke Faskari, jihar Katsina sun gamu da fushin jami’an tsaro.

A yayin musayar wuta da masu tsaron garin, wasu daga cikin ’yan bindigar sun samu munanan raunuka kuma suka tsere zuwa daji.

An ruwaito cewa washegari, mazauna garin sun kama wasu daga cikin raunanan ’yan bindigar su uku kuma suka kashe su nan take.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com