NiMet: Kano, Yobe da Jihohi 30 da Ake Sa Ran Ruwan Sama Zai Sauka Ranar Alhamis

NiMet: Kano, Yobe da Jihohi 30 da Ake Sa Ran Ruwan Sama Zai Sauka Ranar Alhamis

  • NiMet ta fitar da hasashen yanayi na yau Alhamis, 17 ga Yuli, 2025, inda ta nuna yiwuwar samun ruwan sama mai yawa a Arewa
  • Wasu jihohin Arewa za su fuskanci tsawa da ruwan sama mai matsakaicin karfi, yayin da za a samu ruwa kaɗan a Kudancin kasar
  • Hukumar hasashen yanayin ta shawarci jama'a da direbobi su yi taka tsantsan saboda yiwuwar ambaliya, da hatsarin ababen hawa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) ta fitar da hasashen yanayi na yau Alhamis, 17 ga Yulin 2025.

Rahoton ya nuna cewa wasu jihohi za su fuskanci ruwan sama mai yawa, yayin da wasu za su sami ruwan sama kaɗan.

Hukumar NiMet ta ce akwai yiwuwar ruwan sama da tsawa za su sauka a Kano, Yobe da wasu jihohi 30
Ruwan sama mai karfi tare da tsawa yana sauka a wasu sassan Arewacin Najeriya. Hoto: Sani Hamza / Staff
Source: Original

Hukumar NiMet ta fitar da rahoton hasashen yanayin ne a shafinta na X a ranar 16 ga Yulin 2025, kuma ta ce rahoton zai yi aiki ne daga karfe 12:00 na safiya zuwa karfe 11:59 na dare.

Kara karanta wannan

Sun kwanta dama: Buhari, Dantata da wasu manyan ƴan Najeriya da suka rasu a 2025

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hasashen yanayi a jihohin Arewa

Da safiyar yau:

Ana sa ran sararin samaniya zai hade da hadari, amma za a samu bullar rana kaɗan a mafi yawan sassan yankin.

Akwai yiwuwar samun ruwan sama da tsawa mai yawa a sassan jihohin Sokoto, Katsina, Kano, Zamfara, da Kebbi.

Da yamma zuwa dare:

Ana sa ran samun ruwan sama mai matsakaicin ƙarfi tare da tsawa a sassan jihohin Borno, Jigawa, Yobe, Kano, Katsina, Kaduna, Bauchi, Gombe, Taraba, da Adamawa.

Hasashen yanayi a Arewa Tsakiya

Da safiyar yau:

Ana sa ran sararin samaniya zai hade da hadari, amma za a samu bullar rana kaɗan a mafi yawan sassan yankin.

Da yamma zuwa dare:

Ana sa ran ruwan sama zai sauka a sassan babban birnin tarayya (FCT), jihohin Plateau, Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, da Neja.

Hasashen yanayi a jihohin Kudu

Da safiyar yau:

Kara karanta wannan

Bidiyon kalaman Buhari na ƙarshe masu kama hankali yayin da yake barin mulki

Ana sa ran hadari zai hadu sosai sannan a samu ruwan sama kaɗan a sassan jihohin Ekiti, Edo, Delta, Cross River, da Akwa Ibom.

Da yamma zuwa dare:

Ana sa ran ruwan sama kaɗan a sassan jihohin Imo, Abia, Ebonyi, Edo, Anambra, Enugu, Bayelsa, Delta, Rivers, Cross River, da Akwa Ibom.

An shawarci masu ababen hawa da su yi taka tsantsan da tuki yayin da ake ruwan sama
NiMet ta yi hasashen saukar ruwan sama a jihohin Arewa da Kudu a ranar Alhamis. Hoto: Sani Hamza / Staff
Source: Original

Shawarwari da gargadi daga NiMet

An shawarci jama’a da su yi taka tsantsan domin akwai yiwuwar ambaliyar ruwa, hatsarin mota saboda tsawa, iska da kuma ruwa mai ƙarfi.

Hukumar ta kuma shawarci direbobi da su guji yin tuƙi a lokacin ruwan sama mai yawa don gujewa hatsarori.

Hakanan, a guji neman mafaka a ƙarƙashin bishiyoyi yayin guguwa saboda yiwuwar faɗuwar rassan bishiyoyin.

Hukumar ta kuma shawarci kamfanonin jiragen sama da su sami rahotannin yanayi na filayen jiragen sama da bayanan jirgi daga NiMet don tafiye-tafiye cikin aminci.

Malamai sun kira sallar rokon ruwa a Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa, malaman addinin Musulunci a Kano sun yi kira ga al'umma da su fito sallar neman ruwan sama, sakamakon ƙarancin ruwan da ake fuskanta.

Kara karanta wannan

NiMet: Za a sha ruwa da tsawa a Kano, Yobe da jihohin Arewa 13 a ranar Lahadi

Sheikh Ibrahim Khaleel, shugaban majalisar malamai ta jihar Kano ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Legit Hausa ta fahimci cewa Musulmi sun fito sallar roƙon ruwan tun a ranar ranar Asabar da ta gabata domin neman taimakon Allah game da daminar bana.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com