Yan Bindiga: Limami a Uromi da Aka Kashe Hausawa Ya Ƙaryata Rahoton Ƴan Sanda

Yan Bindiga: Limami a Uromi da Aka Kashe Hausawa Ya Ƙaryata Rahoton Ƴan Sanda

  • Babban limamin masallacin Juma'a na Uromi, Imam Muhammad Murtadha Obhakhobo ya karyata rahoton yan sanda
  • Malamin ya ce ya biya N6.5m kudin fansa, ba 'yan sanda suka ceto shi ba daga hannun yan bindiga
  • Limamin ya ce an sace shi ne a kan titin Ubiaja-Illushi ranar 9 ga Yuli, kuma an sako shi ranar 13 bayan an biya kudin fansa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Uromi, Edo - Babban limamin masallacin Juma’a na garin Uromi a jihar Edo, Imam Muhammad Murtadha Obhakhobo ya magantu bayan kubuta daga yan bindiga.

Malamin ya musanta ikirarin cewa ‘yan sanda ne suka ceto shi bayan sace shi da yan bindiga suka yi.

Malamin Musulunci ya ƙaryata yan sanda bayan tsira daga yan bindiga
Limami a Edo ya ƙaryata rahoton ƴan sanda cewa sun kwato shi. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Twitter

Rahoton Vanguard ya ce malamin ya bayyana cewa sai da ya biya N6.5m kafin yan bindigar suka sako shi.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sace malamin addinin musulunci, sun bukaci N30m

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abin da yan bindiga suka nema daga limamin

Legit Hausa ta ruwaito cewa an sace limamin ne a Uromi ranar 9 ga Yuli, inda masu garkuwar suka nemi a biya kudin fansa N30m.

Miyagun sun sace malamin ne jim kaɗan bayan da ya kammala sallar Azahar a ranar Lahadi 13 ga watan Yulin 2025.

Majiyoyi sun bayyana cewa tuni har sun kira iyalansa inda suka nemi a ba su maƙudan kuɗaɗen fansa.

Yan sanda sun ce sun ceto limami

Mai magana da yawun rundunar a Edo, CSP Moses Yamu, ya ce sun samu nasarar ceto limamin bayan matsin lamba da suka rika yi.

Hakan ya sa limamin fayyace gaskiyar abin da ya faru sabanin abin da yan sanda suka ce a cikin wata sanarwa, cewar The Guardian.

Amma a lokacin wata tattaunawa da manema labarai, limamin ya ce akasin hakan ne, domin kuwa sai da ya biya kudin fansa kafin a sako shi.

Kara karanta wannan

"Wa ya kashe man inji?": An gano abin da ya jawo jirgin Air India ya yi hatsari

Ya ce:

“Ni ne Imam Muhammad Murtadha Obhakhobo, babban limamin masallacin Juma’a na Uromi a Edo an sace ni ranar 9 ga Yuli, 2025 a kan titin Ubiaja-Illushi.
“Na kubuta ne bayan na biya Naira miliyan 6.5 ranar 13 ga Yuli, amma sai na ji a labarai cewa wai ‘yan sanda ne suka cece ni."
Limami ya ƙaryata rahoton yan sanda a Edo
Limami a Edo ya ƙaryata ƴan sanda cewa sun kwato shi daga yan bindiga. Hoto: Uromi Esan.
Source: Facebook

Yan bindiga: Limami ya soki azarbabin yan sanda

Limamin ya ce bayan dawowarsa daga hannun masu garkuwa, shugaban sashen ‘yan sanda na Uromi ya ziyarce shi domin jin bayani, wanda ya ba su.

Ya ce bayan ya bayyana wa DPO yadda abin ya faru, sai kawai ya ga ‘yan sanda na neman daukar lamban yabo ba tare da sun yi komai ba.

“An sako ni ne sakamakon kokari na kaina da kuma biyan kudin fansa mai yawa, ba wai saboda kokarin ‘yan sanda ba."

- In ji limamin

Sai dai ya bayyana godiyarsa ga duk wadanda suka yi addu’a da nuna damuwa a lokacin da yake hannun masu garkuwa da mutane.

Kara karanta wannan

An maka Sanusi II a kotu bayan 'umarnin' korar masoyan Aminu Ado daga fadarsa

Yan bindiga sun sace limami a Zamfara

Mun ba ku labarin cewa an tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun sace babban limamin masallacin Juma’a na Faru, Imam Sulaiman Idris da ke karamar hukumar Maradun a Zamfara.

Majiyoyi sun nuna cewa an kama limamin ne da safiya yayin da yake aiki a gonarsa, kuma har yanzu ba a san inda yake ba.

Wani rahoto ya nuna cewa mazauna garin sun bayyana fargaba da fushi, suna kira ga hukumomin tsaro da su dauki mataki cikin gaggawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.