Muhimman Abubuwa 5 da Ya Kamata Musulmi Ya Yi a Ranar Arafah

Muhimman Abubuwa 5 da Ya Kamata Musulmi Ya Yi a Ranar Arafah

  • Ranar Arafah na daya daga cikin ranaku mafi albarka a Musulunci, ana yin azumi da addu’o’i domin samun gafara da rahamar Allah SWT
  • A wani hadisi, Annabi Muhammad (SAW) ya ce azumin ranar Arafah yana goge zunuban shekarar baya da ta gaba
  • Ana son Musulmi su tashi kafin asuba su yi Tahajjud da addu’a, haka nan, a fara shirye-shiryen layya domin cika wannan ibada mai girma

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ranar Arafah, wadda take rana ta 9 ga watan Dhul Hijjah, na daya daga cikin mafiya tsarki a Musulunci, tana ba da dama ga ibada da neman gafara.

Musulmi a fadin duniya, ko suna aikin Hajji ko a’a, suna keɓe wannan rana don addu’a da ambaton Allah domin neman rahama da albarka.

Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Arafah
Muhimman abubuwa 5 da ake son Musulmi ya yi a ranar Arafah. Hoto: @HaramainInfo.
Source: Twitter

Muhimman abubuwa da ake yi a ranar Arafah

Kara karanta wannan

Saura kiris a fara ibadar hajji, Alhajin Kano ya kwanta dama a Saudiyya

Akwai muhimman abubuwa guda biyar da ya dace a yi domin samun lada mai yawa a wannan rana mai albarka da kusanci da Allah, cewar rahoton Islamic Relief UK.

A ranar Arafah mahajjata suna tsayawa a filin Arafah suna addu’a da neman rahamar Allah, wadanda ba su yi Hajji ba su kara yawaita ibada da neman gafara.

Legit Hausa ta duba jerin abubuwan da ya kamata a yi a ranar Arafah:

1. Azumi a ranar Arafah

Azumi a ranar Arfah Sunnah ne mai karfi ga wadanda ba su yin Hajji. Annabi Muhammad (SAW) ya ce:

“Azumin ranar Arfah yana goge zunuban shekara da ta gabata da kuma ta gaba."

Wannan ibada na daga cikin hanyoyin samun yardar Allah da gafararsa, wanda ya yi azumi a wannan rana yana samun rahamar Allah SWT, komai yawan zunubansa.

2. Yin addu’a da neman gafara

Ranar Arfah dama ce ta musamman wajen addu’a, Annabi Muhammad (SAW) ya ce a hadisin Tirmidhi:

“Mafi kyawun addu’a ita ce ta ranar Arfah."

Haka kuma, Allah ya yi umarni a cikin Alkur’ani:

Kara karanta wannan

Ta'addanci: Jagororin Fulani sun nemi a tattauna, an sako Turji cikin masu neman sulhu

"Ku ambaci Allah a cikin kwanaki da aka kayyade.” — Surar Al-Baqarah | 2:203

Ana son Musulmi su ware lokaci don addu’a mai yawa, neman rahama, shiriya da gafarar Allah.

Abubuwa muhimmai game da ranar Arafah
Muhimman abubuwa da Musulmi ya kamata ya yi a ranar Arafah. Hoto: Imran Sham/GettyImages.
Source: Getty Images

3. Yawaita zikiri da ibada ranar Arafah

Ambaton Allah da zikiri yana da matukar muhimmanci a wannan rana, mafi kyawun nau’in zikiri sun hada da:

Zikiri (Laa ilaaha il-lal-laah)

Kabbara (Allahu Akbar)

Godiya (Alhamdulillaah)

Tasbihi (Subhanallaah)

Sunnah ce a yawaita fadar wadannan a ranar Arafah, idin babbar sallah da kwanaki masu zuwa na Dhul Hijjah.

Musulmi su yawaita karatun Alkur’ani, sallolin Nafila da salati ga Annabi (SAW), cewar rahoton Muslim Aid.

4. Shirin layya

Ko da yake ana yanka layya daga 10 zuwa 12 ga Dhul Hijjah, ana fara shiri tun ranar Arafah.

A cewar Mazhabin Hanafi, layya wajibi ne ga baligi, mai hankali wanda ke da dukiya fiye da bukatunsa na yau da kullum.

Abu Dawud ya ruwaito:

“Annabi ya yanka hadaya a Ranar Hadaya. Ya ce: ‘Na juya fuskata ga mahaliccin sammai da kasa, akan addinin Ibrahim, ina bauta wa Allah kaɗai… Lallai salla ta, da ibada ta, da rayuwa ta da mutuwa ta, duk domin Allah Ubangijin Halittu ne.’”

Kara karanta wannan

APC ta haɗa Atiku, El-Rufai da Amaechi, ta yi masu kaca kaca saboda taba Tinubu

Musulmi su tabbata sun shirya hadayarsu kafin idi don cika wannan ibada mai daraja.

Muhimmancin ranar Arafah ga Musulmi
Abubuwa 5 da masu muhimmanci ga Musulmi a ranar Arafah. Hoto: Legit.
Source: Original

5. Tashi kafin asuba domin tahajjud

Wani lokaci mai albarka shi ne kashi na karshe na dare, Annabi Muhammad (SAW) ya ce:

“An tambaye shi wane addu’a ne ake amsawa, sai ya ce: ‘A cikin kashi na karshe na dare, da bayan sallolin farilla.’” — Hadisi | Tirmidhi, 3499

Ana son Musulmi su tashi kafin asuba su ci sahur su kuma yi sallar Tahajjud. Wannan lokaci ne da ya dace wajen neman rahama da gafarar Allah ta hanyar addu’a mai tsanani.

Dokokin ranar Arafah

Mahajjata ba su yin azumi a wannan rana, suna zuwa filin Arafah, suna tsayuwa har zuwa faduwar rana, suna fuskantar alkibla da addu’a na neman gafara.

Annabi (SAW) ya ce:

“Hajji shi ne Arafah.”

Ga wadanda ba sa Hajji, azumi yana da matukar lada kuma Sunnah ne, Musulmi su yi amfani da wannan rana wajen yawaita ibada da neman rahamar Allah.

Ta hanyar aiwatar da wadannan abubuwa guda biyar, Musulmi za su kara kusanci da Allah da kuma shiri don albarkar idin babbar sallah.

Kara karanta wannan

Ambaliya: Buhari ya girgiza da mutuwar mutane kusan 200 a Kano da Neja

Saudiyya ta hana ɗaukar hotuna yayin ibada

Mun ba ku labarin cewa hukumomi a ƙasar Saudiyya ta hana daukar hoto da rera wakoki ko daga tutoci a wuraren ibada yayin aikin Hajji.

Ma'aikatar harkokin cikin gida ta ce haramun ne yin hoto da waya ko kayan daukar hoto a Masallacin Harami, Madina, Mina, Arafat da kuma Muzdalifa

Gwamnatin kasar Saudiyya ta ce aikin Hajji lokaci ne na ibada da hadin kai, kuma za a hukunta duk wanda ya karya doka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.