Sanusi II Ya Naɗa Sabon Turakin Kano yayin da Ɗansa Ya Ziyarci Shugaban APC

Sanusi II Ya Naɗa Sabon Turakin Kano yayin da Ɗansa Ya Ziyarci Shugaban APC

  • Ko da yake rikicin masarautu bai kare ba a Kano, Sarki Muhammadu Sanusi II ya ci gaba da nade-naden sarauta a fadar jihar
  • Sanusi II ya nada sabon Galadiman Kano domin maye gurbin marigayi Abbas Sanusi, kuma ya nada Mahmud Ado Bayero a matsayin Turakin Kano
  • Tafidan Kano, Malam Adam Lamido Sanusi, ya kai ziyara ga Hon. Abdullahi Abbas a ranar Litinin 5 ga watan Mayu, 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Duk da cewa ba a gama da rigimar masarautu ba a Kano, Sarki Muhammadu Sanusi II ya yi nade-nade kamar yadda aka saba.

Nadin baya-bayan nan shi ne na Galadiman Kano domin maye gurbin marigayi, Alhaji Abbas Sanusi da ya riga mu gidan gaskiya.

'Dan Sarki Sanusi II ya ziyarci shugaban APC
Adam Sanusi Lamido ya ziyarci Abdullahi Abbas. Hoto: Sanusi II Dynasty.
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shafin Dala FM Kano ta wallafa a manhajar Facebook a yau Talata 6 ga watabn Mayun 2025.

Kara karanta wannan

Sarki Sanusi II ya isa kasar Tunusia babban taron tattali na Afrika na 2025

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarki Muhammadu Sanusi II ya isa Tunisia

Wannan na zuwa ne bayan Sarki Muhammadu Sanusi II, ya isa kasar Tunisia domin halartar babban taron zuba jari da ciniki na Afrika (FITA2025).

An ce taron zai gudana ne a ranakun 6 zuwa 7 ga watan Mayun shekarar 2025, a babban otal din Radisson Blu da ke birnin Tunis.

Basaraken ya samu rakiyar manyan masu mukamin gargajiya daga Kano, ciki har da Sarkin Shanun Kano, Nazir Halliru, da Jarman Kano.

Adam Sanusi Lamido ya ziyarci shugaban APC

Hakan ya biyo bayan ziyarar da 'dan Sarki Muhammadu Sanusi II ya kai ga shugaban jam'iyyar APC a jihar Kano, Abdullahi Abbas.

Shafin Sanusi II Dynasty ya wallafa a manhajar Facebook cewa Mai girma, Tafidan Kano, Adam Lamido Sanusi ya kai ziyara ta musamman ga shugaban APC a jihar, Hon. Abdullahi Abbas.

Sanarwar ta ce:

"Mai Girma Tafidan Kano, Adam Lamido Sanusi ya ziyarci Hon. Abdullahi Abbas Sanusi a ranar Litinin 5 ga watan Mayun 2025."

Kara karanta wannan

Sanusi II ya halarci nadin sabon Khalifan Tijjaniyya a kasar Burkina Faso

Sarki Sanusi II ya naɗa Turakin Kano
Sanusi II ya sabon Turakin Kano. Hoto: Sanusi II Dynasty.
Source: Twitter

Sarki Sanusi II ya nada Turakin Kano

Sarki Sanusi II ya yi nade-naden ne yayin da shi ma Aminu Ado Bayero ya nada na shi Galadiman Kano a ranar Juma'a 2 ga watan Mayun 2025 da ta gabata.

Daga cikin nade-naden akwai sabon Turakin Kano, Alhaji Mahmud Ado Bayero domin ci gaba da gudanar da sarauta.

A cikin sanarwar, shafin ya ce:

"Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi II Phd, CON ya nada Alh Mahmud Ado Bayero a matsayin sabon Turakin Kano."

Yan sanda sun kulle gidan Galadiman Kano

A baya, kun ji cewa rundunar ‘yan sanda ta mamaye gidan Galadiman Kano da ke Galadanci, a Gwale, bayan naɗa Galadima biyu da aka yi a ranar Juma'a 2 ga watan Mayun 2025.

Sarki Muhammadu Sanusi II ya nada Munir Sanusi Bayero a Gidan Rumfa, yayin da Aminu Ado Bayero ya nada Sanusi Ado Bayero a Nasarawa.

Iyalan gidan Galadima sun ce ba su da hannu a rikicin, amma suna cikin damuwa kan yadda siyasa ke rushe musu zumunci da al’ada.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.