Kotu Ta Bukaci FBI ta Kwancewa Tinubu Zani a Kasuwa kan Zargin Safarar Ƙwayoyi

Kotu Ta Bukaci FBI ta Kwancewa Tinubu Zani a Kasuwa kan Zargin Safarar Ƙwayoyi

  • Wata kotu a Amurka ta umurci hukumar FBI da DEA su saki bayanan binciken da suka shafi Bola Tinubu kan zargin safarar miyagun kwayoyi
  • Kotun ta ce bayanan da mai bincike Aaron Greenspan ya nema ta FOIA sun shafi Tinubu da wasu mutane uku da ke da alaƙa da zargin
  • Hukumar FBI da DEA sun ce ba za su tabbatar ko musanta wanzuwar bayanan ba, amma kotu ta ce hakan ba daidai ba ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Columbia, USA - Wata kotun tarayya da ke Columbia a Amurka ta umurci fitar da bayanan bincike kan Shugaba Bola Tinubu.

Kotu ta umarci FBI da DEA su saki bayanan binciken laifuka da suka shafi Bola Tinubu kan zargin safarar miyagun kwayoyi.

Kotu ta bukaci bankado bayanai kan zargin Tinubu a Amurka
Kotu ta umarci fito da bayanai kan zarge-zargen Tinubu game da safarar miyagun kwayoyi. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Federal Bureau of Investigation, FBI.
Asali: Twitter

Buƙatar kotun Amurka game da zarge-zarge kan Tinubu

Kara karanta wannan

Bayan Atiku ya gana da Buhari, an karfafawa Uba Sani, Tinubu guiwa a 2027

Alkalin kotun, Beryl Howell shi ya bayar da wannan hukunci a ranar 8 ga Afrilun 2025, cewar rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya umurci hukumomin su nemo su kuma sarrafa duk bayanan da ba su da kariya daga FOIA.

Aaron Greenspan, wanda ya kafa dandalin PlainSite, ya shigar da bukatun neman bayanai 12 daga 2022 zuwa 2023.

Bukatar Greenspan ta haɗa da bayanan Tinubu da wasu mutum uku: Lee Andrew Edwards, Mueez Abegboyega Akande da Abiodun Agbele.

FBI da DEA sun yi amfani da “Glomar response” wato ƙin tabbatarwa ko musanta wanzuwar bayanan, amma kotu ta ce hakan bai dace ba a wannan lamari.

An umurci FBI da DEA su gudanar da bincike kuma su saki duk wani bayani da ba ya ƙarƙashin kariya, sannan su kai rahoto zuwa kotu kafin 2 ga Mayu, 2025.

Hukuncin kotu ya ce:

“FBI da DEA sun tabbatar da cewa an gudanar da bincike kan Tinubu dangane da ƙungiyar safarar miyagun kwayoyi.

Kara karanta wannan

Sabuwar wakar caccakar Tinubu ta tayar da kura a Najeriya

“Kowane hakkin sirri da ake tunanin yana tattare da bayanan FBI da DEA kan Tinubu, ya faɗi gaban bukatar jama’a ga sakin irin waɗannan bayanai.
“Tunda FBI da DEA ba su bayar da hujjar kare sirri kan cewa Tinubu yana ƙarƙashin binciken laifi ba, ba su iya kare amsar Glomar ba.”
Kotun Amurka ta taso Tinubu a gaba
Kotu a Amurka ta bukaci bankado bayanai kan zargin Tinubu da safarar kwayoyi. Hoto: Bayo Onanuga.
Asali: Facebook

Abin da alkali ya ce kan lamarin

Kotu ta yarda da amsar CIA ta Glomar, bayan Greenspan ya amince cewa hukumar ta bayyana wanzuwar wasu bayanai masu alaƙa da bukatarsa, cewar Premium Times.

Alkali ya yanke hukunci cewa:

“Duk bayanin da aka tattauna a sama, mai shigar da ƙara ya cancanci samun hukuncin cin nasara kan amsoshin Glomar daga FBI da DEA.
“Saboda haka, FBI da DEA dole ne su gudanar da bincike kuma su sarrafa duk wani bayani da ba ya ƙarƙashin kariya da ya shafi FOIA.

Tinubu ya fara daƙile masu shirin komawa SDP

Kun ji cewa Bola Tinubu na kokarin hana manyan ‘yan siyasa daga bangaren CPC ficewa daga jam’iyyar APC zuwa SDP kafin zaben 2027.

Kara karanta wannan

Turji ya sauya salo, an gano ƴan ta'adda na shiga Sokoto daga dazukan Zamfara

An ce an shirya bai wa Sanata Tanko Al-Makura shugabancin jam’iyya don ya lallaso Buhari da magoya bayansa su ci gaba da kasancewa a APC.

Hakan ya zo bayan manyan jiga-jigan siyasa kamar Atiku, El-Rufai, Tambuwal na tattaunawa da Muhammadu Buhari kan barin APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.