Abin da 'Yan Najeriya ke Cewa bayan Tinubu Ya Cire Mele Kyari daga Shugabancin NNPCL
- Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi sauyin shugabanci a kamfanin mai na ƙasa (NNPCL) ranar Talata, 2 ga watan Maris 2025
- Mai girma Bola Tinubu ya sauya Mele Kyari daga shugabancin NNPCL tare da maye gurbinsa da Injiniya Bashir Bayo Ajulari
- Ƴan Najeriya sun bayyana mabanbantan ra'ayoyi kan wannan sauyin shugabancin da shugaba Bola Tinubu ya yi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sauke Mele Kolo Kyari daga shugabancin kamfanin mai na ƙasa (NNPCL).
Shugaba Tinubu ya kuma sauya kwamitin gudanarwa na kamfanin NNPCL a cikin sauye-sauyen da ya ya amince da su.

Asali: Twitter
Bola Tinubu ya yi sauye-sauye a NNPCL
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaba Bola Tinubu ya kuma maye gurbin Mele Kyari da Injiniya Bayo Ajulari a matsayin sabon shugaban kamfanin NNPCL.
Mai girma Tinubu ya kuma naɗa Ahmadu Musa Kida wanda ya fito daga jihar Borno a matsayin sabon shugaban kwamitin NNPCL.
Ƴan Najeriya sun yi martani kan sauke Mele Kyari
Ƴan Najeriya sun yi martani kan sauyin shugabancin da Shugaba Tinubu ya yi a kamfanin NNPCL.
Waɗanda suka yi magana kan sauyin shugabancin da aka samu a NNPCL sun bayyana mabambanta ra'ayoyi.
Ga wasu daga ciki a nan ƙasa:
Olaudah Equiano:
"Ta tabbata ana maida ƙasar nan ta Yarabawa. Muna taya ka murna shugaban ƙasa."
Kakanfo:
"Wani Bashir Ojulari daga Arewa kuma. Me yasa Shugaba Tinubu ke maida Najeriya ta zama ta Arewa?"
Oladipo E.I:
"Yaushe za a kama Mele Kyari kamar yadda aka kama Emefiele, wanda ake tsare da shi?"
Prosper Kalabar:
"Tuni dama ya kamata a kori Mele Kyari."

Kara karanta wannan
Tinubu ya fadi dalilin da ya sa ya ki daukar shawara, ya nada mai sukarsa minista
Nda Aaron:
"Mele Kyari ya na nan tun zamanin Buhari daga Arewa, don haka ba adalci ba ne sake naɗa wani ɗan Arewa a matsayin shugaban NNPCL. Ɗan Kudu ya dace a naɗa."
Akinnefisi Olamide:
"Wannan abu ne da ya kamata a yi tuntuni, amma dai Kyari ya yi ƙoƙari a mulkinsa wajen farfaɗo da matatun mai."
Haywhy Lenzo:
"Daga ƙarshe, Mele Kyari ya tafi da ƙananun uzurorin da ya daɗe yana badawa tsawon shekaru. Muna taya murna ga sababbin waɗanda aka naɗa."

Asali: Facebook
Benjamin Usende:
"Mu na taya murna! Muƙamin da aka ba Arewa Ta Tsakiya ma Bayerabe aka ba daga jihar Kwara kenan. Me yasa ba a ba wasu ƙabilu don daidaita lamarin ba? Wannan ba daidai ba ne."
Mallam Na Bakin Kogi:
"Ya kasa shirya gasar Al-Qur’ani."
NNPCL ya kawo cikas a yarjejeniyarsa da Dangote
A wani labarin kuma, kun ji cewa kamfanin mai na ƙasa (NNPCL), ya ɗakatar da yarjejeniyar siyar da man fetur a Naira ga matatun cikin gida.
Kamfanin na NNPC ya dakatar da siyar da ɗanyen man fetur ga matatun cikin gida har da ta kamfanin Dangote.
Wannan matakin ana kallonsa a matsayin wani abin da zai iya sanyawa farashin man fetur ya yi tashin gwauron zabi a ƙasar nan.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng