Dubu Ta Cika: Sojoji na tsaka da Farautar Bello Turji, an Cafke Hatsabiban Ƴan Bindiga 2

Dubu Ta Cika: Sojoji na tsaka da Farautar Bello Turji, an Cafke Hatsabiban Ƴan Bindiga 2

  • Dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar kama wasu kasurguman ƴan bindiga biyu da dillalin makamai a jihohin Zamfara da Sakkwato
  • Mai magana da yawun rundunar tsaro na kasa, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana hakan a taron manema labarai ranar Alhamis
  • Ya ce sojojin sun samu nasarori da dama a yaƙi da ƴan tada ƙayar baya a makon da ya shige daga ranar 15 zuwa 20 ga watan Maris, 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Yayin da rundunar sojojin Najeriya ke ci gaba da farautar manyan gasurguman ƴan ta'adda irunsu Bello Turji, an samu nasara a jihohin Sokoto da Zamfara.

Dakarun Sojojin Najeriya sun cafke wasu hatsabiban ƴan bindiga guda biyu da dillalin makamai, Shehu Bagiwaye a kananan hukumomin Gudu (Jihar Sokoto) da Gusau (Jihar Zamfara).

Manjo Janar Markus Kangye.
Sojoji sun kama ‘yan Ta’adda 2 da dillalin makamai a jihohin Sokoto da Zamfara Hoto: @DHQNigeria
Asali: Twitter

Daraktan hulɗa da jama'a na rundunar tsaro (DHQ), Manjo Janar Markus Kangye, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a ranar Alhamis, Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya sa labule da 'shugaban riko' na jihar Ribas, bayanai sun fito

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na ɗaya daga cikin nasarorin da dakarun sojin ke ci gaba da samu a yaƙi da ƴan fashin daji da suka addabi jama'a musamman a Arewa maso Yamma.

Sojoji sun miƙa tubabbu ga gwamnati

Bugu da ƙari, kakakin Hedikwatar, Kangye ya ce rundunar ta mika tsofaffin ‘yan ta’adda guda 75 da suka miƙa wuya ga gwamnatin jihar Borno bayan an kammala canza masu tunani.

A cewarsa, daga cikin tubabbun ƴan ta'addan da aka miƙa wa gwamnatin Borno bayan horar da akwai maza bakwai, mata 34 da yara 34.

Ɓarayin mai sun shiga hannu a Najeriya

Ya ci gaba da cewa cikin makon da ya gabata (15-20 ga watan Maris, 2025), sojojin sun kama mutum 23 da ake zargi da satar man fetur tare da kwato kayayyakin da kudinsu ya kai Naira biliyan 461.7.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin sun gano da kuma lalata rijiyoyin haƙo mai na haram guda 42, tankunan ajiya 33, kwale-kwale 28, da haramtattun matatun mai 21.

Kara karanta wannan

An gano inda Gwamna Fubara yake bayan sojoji sun mamaye fadar gwamnatin Ribas

Haka zalika a cewarsa, dakarun ba su tsaya iya nan ba, sun lalata manyan tukwane da ake sarrafa danyen mai ba bisa ƙa'ida ba guda 36.

Dakarun soji.
Sojoji sun samu galaba kan yan bindiga a jihohin Sakkwato da Zamfara Hoto: @DHQNigeria
Asali: Facebook

Makaman da aka ƙwato daga miyagu

Ya ƙara da cewa dakarun sun kwato bindigogi daban-daban ciki har da AK-47, bindigogin da aka ƙera gida, da makamai kamar gurneti (RPG) da sauransu.

Sojojin sun kuma ƙwato harsasai da dama masu nau'in 7.62mm da kuma gurneti masu fashewa watau bama-bamai duk daga hannun ƴan tada ƙayar baya.

Sauran abubuwan da aka kama sun hada da babura, kekunan hawa, wayoyin hannu, da kuma wasu motocin da ake zargin an yi amfani da su wajen aikata miyagun laifuffuka.

Sojoji sun dakile shirin kungiyar ISWAP

A wani labarin, kun ji cewa dakarun haɗin guiwa na rundunar Operation Haɗin Kai sun yi nasara fatattakar mayakan ISWAP da suka yi yunkurin kai hari a Borno.

An ruwaito cewa dakarun sojojin sun fuskanci ƴan ta’addan inda suka yi musayar wuta, lamarin da ya tilasta wa maharan janyewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262