Ribas: An Fallasa Yadda Wike da Gwamnatin Tinubu Suka Kitsa Dakatar da Fubara

Ribas: An Fallasa Yadda Wike da Gwamnatin Tinubu Suka Kitsa Dakatar da Fubara

  • Wani babba a Neja Delta ya bayyana dakatar da gwamnan Ribas a matsayin haramtacce kuma an sabawa kundin tsarin mulki
  • A cewar Cif Anabs Sara Igbe, Ministan Birnin Tarayya, Nyesom Wike, na da hannu dumu-dumu a rikicin da ya jawo dakatar da Simi Fubara
  • Sara-Igbe ya bayyana cewa an kitsa dokar ta-baci domin raunana gwamnan Ribas da tilasta shi ya mika wuya ga gwamnatin tarayya

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Rivers – Babba a yankin Neja Delta, Cif Anabs Sara-Igbe, ya soki dakatar da Gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara.

Ya bayyana cewa dakatar da zababbiyar gwamnati haramtaccen mataki ne wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Tinubu
An zargi Wike da hannu da dakatar da gwamnan Ribas Hoto: Bola Ahmed Tinubu/Nyesom Wike
Asali: Facebook

A hira da ya yi da Arise News a ranar Alhamis, ya yi ikirarin cewa Ministan Birnin Tarayya, Nyesom Wike, na da hannu dumu-dumu a rikicin siyasar da ke gudana a Rivers.

Kara karanta wannan

Fubara: Bayan majalisa, gwamnoni sun kalubalanci Tinubu kan rikicin Rivers

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sara-Igbe ya zargi shugaba Bola Ahmed Tinubu da yin amfani da karfi fiye da wanda kundin tsarin mulki ya ba shi wajen dakatar da zababben gwamna.

Ribas: Sara-Igbe ya fadi illar dokar ta baci

Cif Sara-Igbe ya kuma bayyana cewa ayyana dokar ta-baci a jihar abu ne da aka shirya tun farko don raunana Gwamna Fubara da tilasta shi ya mika wuya.

Tinubu
Dattijo a Ribas ya zargi gwamnati da kokarin raunana gwamnatin Ribas Hoto: Bola Ahmed Tinubu/Sir Siminalayi Fubara
Asali: Facebook

Sara-Igbe ya soki yadda aka tura jami’an tsaro masu yawa yayin ziyarar Wike a jihar, ya na mai cewa hakan an yi shi ne domin haddasa fargaba da neman halatta dokar ta-baci.

Ya ce:

“Dakatar da Fubara mataki ne da ba bisa doka ba. Kundin tsarin mulki bai bai wa shugaban kasa ikon yin hakan ba.”
“Ministan ya zo Ribas da sojoji, ‘yan sanda, jiragen yaki, DSS, da manyan makamai, duk don wata ziyarar aiki. Manufar ita ce a haddasa tashin hankali domin a sami hujjar ayyana dokar ta-baci.”

Kara karanta wannan

Fubara: Atiku, El Rufai, Obi da mutanen Buhari sun tunkari Tinubu da murya daya

Dattijo a Ribas ya caccaki gwamnatin Tinubu

Sara-Igbe ya kuma zargi fadar shugaban kasa da fifita gefe guda a cikin rikicin siyasar Ribas, yana mai cewa Shugaba Tinubu bai dauki mataki kan rawar da Wike ke takawa ba.

A cewarsa:

“Idan kai uba ne kuma ‘ya’yanka biyu su na fada, dole ne ka zama adali a tsakaninsu. Ba za ka hukunta guda ba ka bar dayan, musamman wanda ya haddasa matsalar.”

Dattijon ya jaddada cewa babuu wata doka da ta ba Tinubu damar dakatar da gwamna da aka zaba, yana mai yin nuni da sashe na 182, 183, 188, da 189 na kundin tsarin mulkin Najeriya.

El-Rufai aika da sako kan batun Ribas

A baya, mun wallafa cewa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya bukaci shugaba Bola Tinubu da ya janye hukuncin dakatar da zababbun jami’an gwamnati a Jihar Ribas.

Ya bayyana cewa wannan mataki ya sabawa doka kuma barazana ce ga tsarin dimokuradiyyar Najeriya, saboda haka dole ne a dauki matakin soke dokar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng