'Yan Bindiga Sun Harbi Malamin Addini, Sun Sace Mutum 6 Suna Tsaka da Yin Ibada

'Yan Bindiga Sun Harbi Malamin Addini, Sun Sace Mutum 6 Suna Tsaka da Yin Ibada

  • 'Yan bindiga sun farmaki coci a Delta inda suka harbi fasto tare da sace mutum shida, ciki har da masu gadi biyu, yayin taron ibadar dare
  • Matar faston ta bayyana cewa maharan sun bude wuta, lamarin da ya sa mijinta ya rasa yatsunsa biyu bayan harsashi ya samu kafarsa
  • Sai dai, Fasto Steve Victor ya ce tun bayan harin ba a karɓi kira daga masu garkuwa ba, amma jami’an tsaro na kokarin kubutar da su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Delta - 'Yan bindiga sun farmaki cocin Elyon Paradise Ministry da ke Ogwashi-Uku, Delta, yayin taron ibada a daren Juma’a, inda suka harbi fasto tare da sace mutum shida.

An kai harin ne da misalin karfe 10 na dare, kusa da kwalejin jihar Delta, inda suka harbi Apostle Divine Omodia, wanda yanzu yake kwance a asibiti bayan jin raunuka.

Kara karanta wannan

An yi arangama a Niger, dan sanda ya dirkawa jami'ar hukumar NIS bindiga, an tsare wasu

'Yan bindiga sun kai hari cocin Delta, sun harbi fasto da sace mutane 6
'Yan bindiga sun harbi fasto, sun sace mutum 6 da suka kai hari cocin Delta. Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Delta: 'Yan bindiga sun harbi fasto

Wannan farmakin ya haifar da fargaba a yankin, inda mazauna garin ke kira ga hukumomi da su dauki matakin gaggawa domin kubutar da wadanda aka sace, inji Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matar faston, Faith Omodia, ta bayyana yadda lamarin ya faru, tana mai cewa maharan sun bude wuta ba kakkautawa cikin dakin ibadar.

“Ina kwance da jaririna a dakin cocin, sai na ji harbe-harbe. Kafin mu ankara, harsasai sun fara shigowa cikin ginin,” in ji Faith.

'Yan bindigar sun sace mutane shida

Ta ce 'yan bindigar, sun harbi mijinta, Apostle Divine a kafarsa, lamarin da ya kai ga har ya rasa yatsunsa biyu sakamakon harbin.

Faith ta ce:

"Bayan sun bude wuta, 'yan bindigar sun tarwatsa masu ibada, sannan suka tafi da mutum shida, ciki har da masu gadin cocin biyu."

An bayyana sunayen wadanda aka sace kamar haka: Helen Onwuamaeze, Ariyo Emmanuel, Chike Okolo, da Blessing Waye, tare da wasu masu gadi da ba a bayyana sunayensu ba.

Kara karanta wannan

Yadda adawar manyan yan siyasar Najeriya za ta shafi tasirin gwamnatin Tinubu

Fasto ya fadi kokarin da 'yan sanda ke yi

Rundunar 'yan sanda ta magantu kan harin da aka ce an kai cocin Delta
'Yan sanda sun ce ba su da masaniya kan harin da aka kai cocin Delta. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Wani fasto na cocin, Steve Victor Onuchukwu, ya fadawa jaridar The Guardian cewa tun bayan harin, masu garkuwar ba su tuntubi kowa ba domin neman kudin fansa.

Ya ce an riga an shigar da rahoton lamarin ga 'yan sanda, amma har yanzu ba a sami sakamako mai kyau ba.

Sai dai Steve Victor Onuchukwu ya ce wani jami’in tsaro ya sanar da shi cewa ana aiki tukuru domin ganin an kubutar da su.

'Yan sanda sun ce basu da labari

Har ila yau, akwai fargaba kan lafiyar Apostle Omodia, wanda aka yi wa tiyata a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba, inda likitoci ke kokarin ceton rayuwarsa.

"Mun garzaya da shi asibiti. A halin yanzu yana cikin dakin tiyata, likitoci na kokarin tabbatar da cewa an ceto rayuwarsa," in ji Onuchukwu.

A halin yanzu, rundunar 'yan sandan Delta ba ta tabbatar da afkuwar lamarin ba.

Kara karanta wannan

'Ya aikata laifuffuka 5': An gurfanar da fitaccen mawakin Najeriya a gaban kotu

Da aka tuntube shi, kakakin rundunar, Bright Edafe, ya ce: “Babu wani rahoto da aka kai wa ‘yan sanda kan wannan harin.”

'Yan bindiga sun kashe fato, sun sace 19

A wani labarin, mun ruwaito cewa, 'yan bindiga sun kai farmaki a Jihar Neja, inda suka kashe wani fasto tare da yin garkuwa da akalla mutane 19 kafin su tsere.

Kamar yadda suka saba kai hare-hare a kauyuka, sun kutsa cikin garuruwan Ogu da Tegina da ke Karamar Hukumar Rafi dauke da babura masu yawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.