Tinubu Ya Amince a Kafa Sababbin Jami'o'in Tarayya a Wasu Jihohi 2, An Fadi Sunaye
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da kafa Jami’ar Fasaha a Iyin Ekiti da Jami’ar Noma a Iragbiji don inganta ilimi da noma a Najeriya
- Jami’ar Iyin Ekiti za ta mayar da hankali kan fasahar zamani, injiniyanci da kimiyyar muhalli don samar da sabbin hanyoyin ci gaba
- Jami’ar Iragbiji za ta bunkasa noma, horas da kwararru, inganta dabarun samar da abinci, da tallafa wa ci gaban tattalin arzikin yankin
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da dokokin da suka kafa sababbin jami’o’in tarayya biyu a Najeriya.
Jami’o’in da aka kafa sun hada da Jami’ar Fasaha da Kimiyyar Muhalli, Iyin Ekiti da Jami’ar Noma da Nazarin Ci Gaba, Iragbiji, Osun.

Asali: Twitter
Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele, ya bayyana amincewa da dokokin a Abuja, a ranar Alhamis, inji rahoton Punch.

Kara karanta wannan
Gwamna Abba zai jiƙa mutanen Kano da ayyukan alheri, ya ware sama da Naira biliyan 30
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Majalisar dattawa ta amince da kudirin dokokin a 2023 da 2024, inda suka samu amincewar majalisar wakilai kafin Shugaba Tinubu ya sanya hannu.
Jami’o’in za su inganta ci gaban Najeriya
Sanata Bamidele ya ce sababbin jami’o’in za su taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban kasa, musamman a fannin fasaha, noma da kare muhalli.
“Ayyukan jami’o’in za su cike gibin ilimi a fannin kimiyya da fasaha, da habaka noma don tabbatar da wadatar abinci a Najeriya,” inji shi.
Ya bayyana amincewar Tinubu da dokokin a matsayin wani mataki mai muhimmanci da zai taimaka wajen shawo kan matsalar karancin abinci da dumamar yanayi.
Gwamnatin tarayya ta goyi bayan sababbin jami’o’in
Ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya ba da shawarar kafa jami’o’in a wata wasika da ya aika wa fadar shugaban kasa a ranar 19 ga Fabrairu.

Asali: Facebook
Ya bayyana cewa Jami’ar Fasaha da Kimiyyar Muhalli, Iyin Ekiti, za ta mayar da hankali kan ilimi da bincike mai dogaro da fasaha.
“Za ta samar da kwararru a fannin injiniyanci, kirkire-kirkiren fasaha da kimiyyar zamani domin bunkasa masana’antu da samar da ayyukan yi,” inji ministan.
Haka kuma, jami’ar za ta rungumi nazarin muhalli da mayar da hankali kan sauyin yanayi, makamashi mai tsafta, da cigaban birane masu dorewa.
Jami’ar Iragbiji za ta taimaka wajen wadatar abinci
Dangane da Jami’ar Noma da Nazarin Ci Gaba, Iragbiji, The Nation ta rahoto Alausa ya ce za ta inganta fasahar noma don bunkasa samar da abinci a Najeriya.
Ministan ya ce:
“Za ta karfafa sabbin dabarun noma, sarrafa amfanin gona, da kirkirar hanyoyin noma masu jure sauyin yanayi don bunkasa samar da abinci."
"Za ta hada ilimin noma da nazarin ci gaban al’umma, don horar da kwararru da za su taimaka wajen magance matsalolin karkara.
"Haka kuma, jami’ar za ta bunkasa kasuwancin noma da horas da dalibai kan sana’o’in da za su iya dogaro da kai."
A cewar Alausa, jami’ar za ta inganta tattalin arzikin Iragbiji da kewaye, ta hanyar samar da ayyukan yi da bunkasa kasuwanci.
Tinubu ya ki amincewa a kafa jami'a a Adamawa
A wani labarin, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ƙi amincewa da dokar kafa sabuwar jami’ar ilmi ta tarayya a garin Numan da ke jihar Adamawa.
Wannan mataki na nufin cewa ba za a kafa jami’ar ba, duk da shirin da aka tsara don inganta ilimi a yankin, wanda wasu ke ganin zai jawo koma baya a jihar.
Asali: Legit.ng