Tsohon Gwamna Ya Hadu da Mutumin da Ya So Kashe Shi a 2006, An Ji Me Ya Fada Masa

Tsohon Gwamna Ya Hadu da Mutumin da Ya So Kashe Shi a 2006, An Ji Me Ya Fada Masa

  • Rauf Aregbesola ya yafe wa Sikiru Olaboye, wanda ya nemi gafararsa bayan an zarge shi da yunƙurin kashe shi a 2006 a Osogbo
  • Tsohon gwamnan ya ce bai rike Sikiru ko wadanda suka dauki nauyin harin ba, yayin da ya yiwa mutumin nasiha mai ratsa zuciya
  • Aregbesola ya zama gwamnan Osun a 2010 bayan kotu ta soke nasarar Olagunsoye Oyinlola, wanda INEC ta ba nasara a 2027

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Osun - Tsohon gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, ya gana da Sikiru Olaboye, wanda ake zargi da yunƙurin kashe shi a bikin ranar Oroki na 2006.

A ranar Lahadi, Aregbesola ya bayyana cewa ya yafe wa Olaboye, kuma baya da wata ƙiyayya ga waɗanda suka shirya wannan hari.

Tsohon gwamnan Osun ya yi magana da ya hadu da wanda ya so kashe shi a 2006
Tsohon gwamnan Osun, Aregbesola ya yafewa mutumin da ya so kashe shi a 2006. Hoto: @raufaregbesola
Asali: Twitter

A sakon da ya wallafa a shafinsa na X, tsohon gwamnan ya ce an faɗa masa cewa Olaboye ya kira wani gidan rediyo a Osogbo domin neman gafararsa.

Kara karanta wannan

'Akwai fa'ida sasantawa da Tinubu': Dan majalisar PDP ya shawarci tsohon gwamna a APC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Aregbesola ya yafewa wanda ya so kashe shi

“A yau, na karɓi Sikiru Olaboye, wanda ya yi yunƙurin kashe ni a bikin Oroki Day na 2006 a Osogbo,” in ji Aregbesola.

Tsohon gwamnan na Osun ya ci gaba da cewa:

“An faɗa mani cewa ya kira gidan rediyo a Osogbo makonnin da suka wuce domin neman gafarata.
“A yau, yayin da nake masa nasiha, na tabbatar masa cewa ban ɗauki wani zafi a zuciyata ba kuma ban nemi ramuwar gayya ba.
“Allah ne kaɗai ke da ikon yin gafara, kuma ina addu’a ya gafarta mana baki daya.”

Harin da aka kai wa Aregbesola a 2006

Rahoton The Cable ya nuna cewa ana gudanar da bikin ranar Oroki a kowace shekara, inda mutanen Osogbo ke taruwa domin ƙarfafa haɗin kai da zumunci.

A ranar 5 ga Agusta, 2006, ‘yan daba da ake zargin magoya bayan Gwamna Olagunsoye Oyinlola ne suka kai wa Aregbesola hari.

Kara karanta wannan

'Munafurcin siyasa ba na irinmu ba ne': El Rufai ya sake ta da kura, ya jaddada matsayarsa

Farmakin ya jawo an lalata aƙalla motoci shida tare da jikkata mutane da dama, a lokacin da zaben gwamna na 2007 ke gabatowa.

Hukumar INEC ta ayyana Oyinlola a matsayin wanda ya lashe zaben, amma kotun daukaka kara ta kwace kujerar tare da ayyana Aregbesola a matsayin gwamna a 2010.

Duba hotunan haduwar Aregbesola da Sikiru a kasa:

Kungiyar Aregbesola ta fice daga APC

A wani labarin, mun ruwaito cewa, kungiyar Omoluabi ta tsohon gwamnan Osun ta fice daga APC gabanin zaɓen gwamna na 2026.

Sakataren kungiyar ya ce rikice-rikicen cikin gida da rashin shugabanci nagari sun raunana APC a jihar Osun.

Rauf Aregbesola ya yaba wa mambobi bisa jajircewarsu, yana mai bayyana amfanin ficewarsu daga jam’iyyar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

iiq_pixel