'A kan Titi Muke Kwana': Wata Zanga Zanga Ta Barke a Sokoto saboda Shirin Rusa Gidaje

'A kan Titi Muke Kwana': Wata Zanga Zanga Ta Barke a Sokoto saboda Shirin Rusa Gidaje

  • Gomman mutane maza da mata ne suka kaddamar da zanga zangar adawa da gwamnatin jihar Sokoto a ranar Talata, 22 ga Oktoba
  • Masu zanga zangar sun zargi gwamnatin Sokoto da korarsu daga gidajen da suka shafe shekara da shekaru suna rayuwa a ciki
  • An rahoto cewa gwamnati ta kori mazauna rukunin gidaje na Yauri Plats a makon jiya, lamarin da ya tilastawa wasu kwana a titi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Sokoto - Mazauna rukunin gidaje na Yauri Plats da ke Sokoto sun gudanar da zanga zangar lumana domin nuna adawa da matakin gwamnatin jihar.

An ga gomman mazauna Yauri Plats a ranar Talata suna zanga zanga kan korarsu daga rukunin gidajen da gwamnatin jihar ta yi.

Kara karanta wannan

NDLEA: Majalisa ta dauki mataki kan zargin kama kwayoyi a gidan sanata

Masu zanga zanga a Sokoto sun yi adawa da korarsu daga gidajensu da gwamnatin jihar ta yi
Zanga zanga ta barke a Sokoto kan zargin kwacewa gomman mutane gidaje. Hoto: @Ahmedaliyuskt
Asali: Facebook

Masu zanga-zangar, sun mamaye sakatariyar kungiyar 'yan jarida ta Najeriya dauke da kwalaye da rubuce-rubuce daban-daban inji rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Sokoto za ta rusa Yauri Plats

Masu zanga-zangar dai sun yi zargin cewa korarsu daga gidajen da suka shafe sama da shekaru 40 suna zama a ciki ba daidai ba ne.

An tattaro cewa akalla dakuna 180 kowanne mai dauke da akalla mutane shida ne gwamnatin jihar Sokoto ta sanyawa alamar rusawa a rukunin gidaje na Yauri Plats.

Mazauna gidajen da abin ya shafa da suka hada da mata da yara na kwana a filin Allah kusa da rukunin gidajen tun bayan korar da aka yi musu a makon jiya.

Sun yi ikirarin cewa gwamnatin jihar Sokoto ba ta biya diyya ba, kuma ba ta ba su wani wurin kwana kafin a kore su ba.

Kara karanta wannan

Ana rade radin rigimar Abba da Kwankwaso, an kori yan jaridu daga gidan gwamnati

'A titi yanzu muke kwana' - Mazauna

Talatu Yusuf, daya daga cikin mutanen da aka haifa kuma suka girma a rukunin gidajen, ta shaida wa Aminiya cewa tun a 1992 iyayenta ke zama a gidan.

“An kore mu a makon da ya gabata kuma a halin yanzu, ba mu da wani matsugunni. Tun makon da ya gabata muke kwana a filin Allah.”

- A cewar Talatu.

Wata mata mai suna Malama Aisha Bala ta ce ta shafe shekara 21 a gidan da take ciki, ta ce an tilasta musu kwana a kan titi bayan korar su.

Zanga zanga ta barke a Sokoto

A wani labarin, mun ruwaito cewa fusatattun mutane sun gudanar da zanga-zanga kan nisan da 'yan bindiga suka yi wa Sarkin Gobir, Alhaji Isa Muhammad Bawa a jihar Sokoto.

A yayin zanga-zanga a garin Sabon Birni, an ce an yi kone-kone a kan tituna domin nuna adawa da kisan gillar da 'yan bindigan suka yiwa basaraken.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.