Kaduna: An Zargi Sojoji da Sake Jefa Bama Bamai a Masallaci Aka Kashe Bayin Allah

Kaduna: An Zargi Sojoji da Sake Jefa Bama Bamai a Masallaci Aka Kashe Bayin Allah

  • Mazauna kauyuka biyu a jihar Kaduna sun zargi jami'an sojojin saman Najeriya da kai masu hari a masallaci da kasuwa
  • An yi zargin mutane 23 aka gano da su ka hada da manoma da yara bayan kurar harin ta lafa, lamarin da aojojin su ka musanta
  • Mataimakin daraktan yada labaran rundunar, Gruf Kyaftin Kabiru Ali ya yi bayanin cewa an kai harre-haren kan yan ta'adda

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kaduna - Wasu daga cikin mazauna karamar hukumar Giwa da ke jihar Kaduna sun yi zargin jiragen sojojin saman Najeriya sun jefa masu bama-bamai.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kutsa kauyen Ministan tsaro, sun sace 40 da hallaka wasu

Sun ce an jefa bam din a kan wani masallaci da kasuwa, wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane 23 zuwa yanzu.

Kaduna
An zargi sojojin sama da jefa bam Kaduna Hoto: Nigeria Air Force HQ
Asali: Facebook

Jaridar Aminiya ta wallafa cewa mazauna yankunan sun ce an kai harin ne a wani yanayi mai kama da wanda jami'an su ka kai kan mazauna Tudun Biri, inda mutane sama da 100 su ka rasu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gano gawarwaki a harin Kaduna

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa zuwa yanzu, an gano gawarwakin jama'a akalla 23, daga ciki har da manoma da kananan yara.

Mazauna Jika da Kolo a karamar hukumar Giwa da aka kai wa harin sun samu sabani kan ainihin adadin wanda su ka rasu a harin.

Harin Kaduna: Rundunar sojin sama ta wanke kanta

Rundunar sojin saman kasar nan ta yi martani kan zarginta da kai hari kan mazauna karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

'Zai kara aure?': Al'umma sun bayyana ra'ayoyi kan sakin Seaman Abbas

Mataimakin daraktan yada labaran rundunar, Gruf Kyaftin Kabiru Ali ya ce jami'ansu sun kai farmaki kan wurin ajiye makaman yan bindiga a yankin da ke da alaka da Dogo Gide.

Kaduna: Yan bindiga sun kashe dan takara

A wani labarin, mun ruwaito cewa wasu yan ta'adda da ba a san ko su waye ba sun hallaka dan takarar kansila a karamar hukumar Kauru a Kaduna, Raymonda Timothy da kaninsa, James Timothy.

Shugaban karamar hukumar Kauru a Kaduna da ya tabbatar da harin ya nemi daukin jami'an tsaro wajen gano wadanda su ka tafka mummunan aiki, da kare afkuwar haka a gaga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.