Jerin Rikakkun Yan Ta'adda 7 da Gwamnatin Tinubu Ta Yi Nasarar Hallakawa

Jerin Rikakkun Yan Ta'adda 7 da Gwamnatin Tinubu Ta Yi Nasarar Hallakawa

A ranar Juma'a 13 ga watan Satumbar 2024 aka hallaka rikakken dan bindiga, Halilu Sabubu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Kisan dan ta'addan ya sanya farin ciki a zukatan yan Najeriya saboda yadda ya jefa al'umma a halin kunci saboda matsalar tsaro.

Yan bindiga da suka bakunci lahira a mulkin Bola Tinubu
Jerin kasurguman yan bindiga da aka hallaka a mulkin Bola Tinubu. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Twitter

Gwamnatin Bola Tinubu ta yi nasarar hallaka kasurguman yan bindiga da dama wanda suka addabi al'umma musamman a Arewa maso Yamma.

Legit Hausa ta jero muku wadanda aka yi nasarar hallaka su.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Baleri Fakai

Rahotanni sun tabbatar da cewa jami'an tsaro sun yi ajalin Baleri Fakai a yau Litinin 16 ga watan Satumbar 2024.

Kara karanta wannan

Gwamna Dauda ya fadi halin da Turji da yan bindiga ke ciki bayan kisan Halilu Buzu

Baleri ya kasance na hannun daman rikakken dan bindiga, Bello Turji da ya addabi al'umma, kamar yadda Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na X.

2. Halilu Sabubu

Jami'an tsaro sun yi nasarar hallaka dan ta'adda, Halilu Sabubu a ranar Juma'a 13 ga watan Satumbar 2024.

An ayyana Sabubu wanda ake nema ruwa a jallo a watan Mayun 2024 da ta gabata.

3. Ali Kachalla

A ranar 12 ga watan Disambar 2023 aka hallaka Kachalla a karamar hukumar Munya da ke jihar Niger.

4. Dangote

Kasurgumin dan ta'adda, Dangote ya rasa ransa a watan Afrilun 2024 a jihar Katsina.

Dangote ya mutu yayin arangama da tsagin dan ta'adda, Dankarami a dajin karamar hukumar Batsari zuwa Jibia.

5. Damina

A watan Maris na 2024 jami'an sojoji suka yi nasarar hallaka Damina da ya addabi yankin Arewa maso Gabas.

Kara karanta wannan

Rundunar sojoji ta gwangwaje dakarun da suka hallaka dan ta'adda, Halilu Sabubu

6. Modi-Modi

Jami'an tsaro sun samu galaba inda suka hallaka dan ta'adda, Usman Modi-Modi a jihar Katsina.

Rahotanni sun ce an hallaka yan bindiga a fadan da suka hada da Mankare da Gunki Ummadau da Dogo Jabi da Harisu Babba a karamar hukumar Safana.

7. Yellow Jambros

A karshen shekarar 2023 aka hallaka kasurgumin dan ta'adda, Yellow Jambros a jihar Kaduna.

Sojojin saman Najeriya ne suka hallaka Jambros a karamar hukumar Chikun da ke jihar Kaduna.

Bulama ya kafa asusun tallafawa sojoji

Kin ji cewa Lauya Bulama Bukarti ya kaddamar da asusun tallafawa sojoji da suka hallaka Halilu Sabubu a jihar Zamfara.

Bulama ya ce a ƙungiyarsu sun tallafa da kudi har N1.8m domin karfafawa sojojin guiwa tare da nuna musu goyon baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.