Fitaccen Mawaki Musulmi Ya Zabgawa Malamin Addini Mari a Bidiyo, Ya Fadi Dalili

Fitaccen Mawaki Musulmi Ya Zabgawa Malamin Addini Mari a Bidiyo, Ya Fadi Dalili

  • Mawakin Najeriya, Habeeb Olalomi Badmus ya mari wani Fasto da ke wa'azi kusa da shagonsa na siyar da kayan shaye-shaye
  • Mawakin da ake kira Portable ya gargadi Faston da ya bar kusa da shagonsa inda ya ke zargin yana damun abokan huldarsa
  • An yada faifan bidiyon a kafofin sadarwa inda mutane da dama suka goyi bayansa yayin da wasu ke cewa abin da ya yi ya kauce hanya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Lagos - Fitaccen mawaki a Najeriya, Habeeb Olalomi Badmus ya mari wani Fasto saboda wa'azi a wurin kasuwancinsa.

Mawakin da aka fi sani da Portable ya mari Faston ne kan zargin zai kora masa abokan hulda a shagonsa na shaye-shaye.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun sace Bello Yabo? Shehi ya yi maganar 'garkuwa' da shi da 'kamen' DSS

Mawaki ya mari malamin addin saboda wa'azi a wurin kasuwancinsa
Mawaki Portable ya mari wani Fasto da ke wa'azi a shagonsa. Hoto: @portablebaeby.
Asali: Instagram

Yadda mawaki ya mari Fasto saboda wa'azi

An yada bidiyon ne a shafin Instagram wanda ya dauki hankulan mutane da dama da suka tofa albarkacin bakinsu.

An gano Portable na umartan Faston ya bar kusa da shagonsa saboda yana addabar abokan huldarsa a wurin.

Daga bisani mawakin ya tunkari Faston tare da cewa yana damunsa inda ya zabga masa mari.

Portable ya fadawa Faston cewa ya yi addu'a a gida kafin ya fito domin haka babu wanda zai koya masa addu'a.

"Ka zo harkar kasuwanci ne ko ka kawo kudi?, kai mahaukaci ne? ka zo nan kana ta ihu a kai na."
"Kafin na bar gida, na yi addu'a, ku fada masa ya yi gaba, kudi ne muke tsammani a nan."

- Portable

Mawaki ya caccaki masu zanga-zanga a Najeriya

Kara karanta wannan

Shugaban majalisa ya koka da sace mutane a asibitin Kaduna, ya fadi abin da ake bukata

Kun ji cewa Mawaki Habeeb Okikiola ya dira kan masu zanga-zanga inda ya ce talauci da rashin aiki ne yake yaudarar matasan da ke son fita.

Mawakin da aka fi sani da Portable ya ce a baya ya fita zanga-zanga amma lokacin ba shi da ko kwabo amma yanzu ya tsira daga talauci.

Portable yayi wannan martani ne yayin da matasa a Najeriya suka shirya fita zanga-zanga a ranar 1 ga watan Agustan 2024 a kasar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.