Digiri Dan Kwatano: Gwamnati Ta Lissafa Jami’o’in Benin, Togo da Ta Amince da Su

Digiri Dan Kwatano: Gwamnati Ta Lissafa Jami’o’in Benin, Togo da Ta Amince da Su

  • Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta ce akalla dalibai 21,600 ne suka mallaki takardun digiri na bogi daga jami'o'in Benin da Togo
  • Binciken da Najeriyar ke yi na da nufin magance yawaitar digirin bogi da ya girgiza harkar ilimin kasar biyo bayan rahoton kwakwaf
  • Duk da haka, an bayyana cewa ba dukkanin daliban Najeriya a Jamhuriyar Benin da Togo ne ke karatu a jami'o'in da ba a amince da su ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayyana cewa jami’o’i biyar ne kacal a jamhuriyar Benin da uku a Togo aka amince da su a hukumance.

Gwamnatin ta ce wadannan jami'o'in ne kadai aka amince 'yan Najeriya su je su yi karatu a ciki domin samun shaidar kammala digiri.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun yi artabu da miyagu, an sheke 'yan bindiga a Katsina

Ministan ilimi, Tahir Mamman ya yi magana kan digiri dan Kwatano
Gwamnatin tarayya ta fadi sunayen jami'o'in da ta amince da su a Togo da Benin. Hoto: @ProfTahirMamman
Asali: Twitter

Ministan ilimi, Tahir Mamman ne ya bayyana hakan a wata hira da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, 25 ga watan Agusta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An bankado badakalar digirin bogi

Dangane da dakatar da karbar digiri daga Jamhuriyar Benin da Togo bayan badakalar digirin bogi da aka bankado, Mamman ya ce matsalar hadari ce ga kasar.

Tahir Mamman ya jaddada buƙatar kiyaye mutuncin ilimi tare da yin alƙwarin haɗa gwiwa da hukumomin da abin ya shafa domin dawo da martabar tsarin.

Mun ruwaito ministan ya sha alwashin tsaftace fannin ilimi a Najeriya yana mai nuna rashin jin daɗinsa da irin abubuwan da aka bankaɗo a lokacin binciken digirin bogi.

Jami'o'in da aka amince da su

Duba jerin jami'o'in Benin da Togo da ke da lasisin yin digiri a ƙasa:

  1. Jami'ar Abomey-Calavi, Jamhuriyar Benin
  2. Jami'ar Parakou, Jamhuriyar Benin
  3. Jami'ar UNSTIM Abomey
  4. Jami'ar noma ta kasa da ke Jamhuriyar Benin
  5. Jami'ar ADC da ke Jamhuriyar Benin
  6. Jami'ar Lomé, Togo
  7. Jami'ar Kara, Togo
  8. Jami'ar Katolika ta Yammacin Afrika, Lome, Togo

Kara karanta wannan

PDP ta fara shirin hukunta tsohon sanata bayan ya kwance mata zani a kasuwa

Duba cikakken jerin a nan kasa da @Theumar_audu ya wallafa a shafinsa na X:

Jami'o'i 9 da ake bincike a Najeriya

A wani labarin, mun ruwaito cewa hukumar kula da jami'o'i ta kasa (NUC) ta fara gudanar da bincike kan wasu jami'o'in Najeriya tara da ake bincikarsu kan badakalar digirin bogi.

A yayin da hukumar NUC ta lissafa jami'o'in ta kuma ce dukkanin daliban kasar da suka samu digiri daga jami'o'in to ya kuka da kansa har zuwa lokacin da za ta kammala bincike.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.